Sojojin mamayar Isra’ila sun sanar da kaddamar da farmaki kan yankin  kudancin Siriya

Sojojin mamayar Isra’ila sun sanar da cewa: Da sanyin safiyar yau Laraba, jiragen yakinsu suka kaddamar da farmaki kan wasu wuraren soji a kudancin Siriya, kuma sun dora alhakin halin da ake ciki a kan gwamnatin Ahmed al-Sharaa.

Rundunar sojin mamayar Isra’ila a cikin wata sanarwa da ta fitar ta ce: A wani lokaci kadan da ya gabata, bayan kai hare-hare kan yankunan haramtacciyar kasar Isra’ila, jiragen saman yakin na haramtacciyar kasar Isra’ila sun yi ruwan bama-bamai a wuraren makaman gwamnatin Siriya a kudancin kasar ta Siriya.

Ta kara da cewa: Halaltacciyar gwamnati ce ke da alhakin halin da ake ciki a kasar Siriya, kuma za ta ci gaba da daukar nauyinta muddin aka ci gaba da nuna kyama ga yahudawan sahayoniyya daga yankinta, sojojin za su kalubalanci duk wata barazana da ke da hadari ga haramtacciyar kasar Isra’ila.

Tashar yada labarai ta kasar Siriya ta tabbatar da cewa: Jiragen saman Isra’ila sun kaddamar da farmaki a Tal Shaar da ke yankin Quneitra da ke kusa da birnin Izra da ke tsakiyar yankin Dar’a da kuma yankunan Sa’sa’ da Kanaker da ke yankin birnin Damascus fadar mulkin kasar.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Isra ila sun

এছাড়াও পড়ুন:

Sheikh Naim Qassem Da Aragchi Sun Tabbatar Da Kara Karfin Zumunci Tsakanin Iran Da Lebanon

Shugaban kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon Sheikh Nain Qasim da kuma ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi sun gana a birnin Beirut babban birnin kasar Lebanon inda bangarorin biyu suka tattauna al-amuran siyasa da yankin kudancin Asiya tare da kasar Lebanon.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto aragchi yana cewa dangantaka tsakanin Iran da kungiyar Hizbullah dangane ce wacce ta shafi yankin kudancin Asiya gaba daya.

A nashi bangaren shugaban kungiyar Hizbullah sheikh Naem Kassem ya godewa JMI ta irin tallafin da take bayarwa ga kungiyoyi da kasashen kawancen masu gwagwarmaya a yankin wadanda suka hada da Falasdinawa da Lebanon da sauransu.

Aragchi ya kara da cewa Iran a shirye take ta taimakawa kasar Lebanon a harkokin siyasa tattalin arziki da zamantakewa. Ya kuma yabawa kungiyar Hizbullah kan rawan da take takawa wajen tabbatar da tsaro da kuam zaman lafiya a kasar Lebanon, musamman da HKI wacce take mamaye da wasu yankunan na kasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Ben Gurion Na Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Musulman Kudancin Kaduna sun yi taron addu’ar zaman lafiya
  • Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba
  • Sheikh Naim Qassem Da Aragchi Sun Tabbatar Da Kara Karfin Zumunci Tsakanin Iran Da Lebanon
  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Cewa: Amurka Da Isra’ila Suna Da Mugun Nufi Kan Iran Da Kasashen Musulmi
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Ben Gurium Na Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Guardian: Isra’ila Tana Kai Wa Makarantun Dake Dauke Da ‘Yan Gudun Hijira a gaza Hari, Tana Sane Da Hakan
  • Iran Ta Yi Watsi Da Da’awar Kungiyar Hadin Kan Kasashen Larabawa Na Da’awar Mallakar Wasu Yankunan Iran
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Aiwatar Da Wani Kisan Kiyashi Kan Masu Bukatar Kayan Agaji