Iran ta bukaci hadin kan al’ummar Lebanon wajen warware matsalolin kasar
Published: 4th, June 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araghchi ya bukaci hadin kan al’ummar kasar Lebanon wajen warware matsalolin kasar, yana mai kira da a yi shawarwarin kasa tsakanin dukkanin kungiyoyin siyasa domin cimma matsaya daya.
Araghchi ya bayyana haka ne a wata ganawa da ya yi a ranar Talata, da shugaban kasar Labanon, Joseph Aoun a birnin Beirut.
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya jaddada aniyar kasarsa na bunkasa alakarta da kasar Lebanon, bisa mutunta juna.
Ya kuma sanar da cewa, kamfanonin Iran a shirye suke su marawa gwamnatin Lebanon baya a kokarinta na sake gina kasar.
A nasa bangaren shugaba Aoun ya jaddada tsarin gwamnatinsa na bunkasa alaka da dukkan kasashen duniya tare da tabbatar da aniyar kasar Lebanon na kara dankon zumuncin da ke tsakaninta da Iran a fannoni daban daban.
Ya jaddada cewa kawo karshen mamayar wasu sassan kasar Lebanon da kuma gyara barnar da gwamnatin Isra’ila ta yi, su ne manyan abubuwan da sabuwar gwamnatin ta Labanon ta sa a gaba.
Araghchi ya kuma gana da firaministan kasar Lebanon Nawaf Salam, A yayin wannan ganawar, sun yi musayar ra’ayi kan bunkasuwar dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, da kuma ci gaban yankin.
Araghchi ya bayyana ziyarar tasa a matsayin wani bangare na manufofin gwamnatin Iran na karfafa alaka da kasashe makwabta da na shiyya, ciki har da Lebanon.
Kafin hakan dama ya ziyarci kasar Masar, a ci gaba da wannan manufa.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Lebanon Araghchi ya
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Bukaci IAEA Tayi Tir Da Harin Da Isra’ila Ta Kai A Tashoshin Nukiyarta.
Mohammad Islami shugaban hukumar kula da makamashin nukiliya na Iran ta fadi a bayan taron da hukumar ta IAEA dake gudanarwa a Vienna yanzu haka cewa yana neman hukumar ta IAEA ta goyi bayan kudurin da ta fitar kuma ta yi Tir da harin wuce gona iri da hki ta kai kan tashoshin nukiliyarta.
Wakilai guda 180 a hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya ne suka hallara abirnin viyana daga ranar 15-19 domin gudanar da taron kasa da kasa karo na 69 da hukumar ta duniya ke shiriya a hedkwatarta dake Vienna na kasar Austeria
Yace mun bayyana cewa alummar Iran basu da rauni wajen fuskantar duk wata barazana, kuma basu da niyyar mika wuya, ,ya kara da cewa ilimin nukiliyar Iran na asalai ne kuma ba zaa iya share shi ta hanyar tayar da bama bamai ba.
.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana September 16, 2025 Pezeshkian: Saudiyya Na Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Samar Da Hadin Kan Kasashen Musulmi September 16, 2025 Pezeshkian: Ta’addancin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Kan Kasar Qatar Zalunci Ne Ga Diflomasiyya September 16, 2025 Baqa’i: Kowace Kasa A Duniya Tana Da Hakkin Mallakar Makamashin Nukiliya Na Zaman Lafiya September 16, 2025 Kungiyar Human Rights Watch; Isra’ila Ta Kashe ‘Yan Jarida Fiye Da 30 A Kasar Yemen Ne Da Gangan September 16, 2025 Kungiyar Kare Hakkokin Bil’Adama Ta Siriya Ta Bankado Karin Fararen Hula Da Aka Kashe A Rikicin Suweida September 16, 2025 Tawagar Yan Wasan Damben Gargajiya Ta Iran Ta Zama Zakara A Damben Ta Duniya September 16, 2025 An Fara Taron Hukumar Makamashin Nukliya Ta Duniya IAEA Karo Na 69 A Birnin Vienna September 16, 2025 Espania Ta Soke Cinikin Makamai Na EUR Miliyon 700 Da HKI Saboda Kissan Kiyashi A Gaza September 16, 2025 Makaman ‘Drons’ Na Yemen Sun Fada Kan Wurare Masu Muhimmanci A HKI September 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci