Iran ta bukaci hadin kan al’ummar Lebanon wajen warware matsalolin kasar
Published: 4th, June 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araghchi ya bukaci hadin kan al’ummar kasar Lebanon wajen warware matsalolin kasar, yana mai kira da a yi shawarwarin kasa tsakanin dukkanin kungiyoyin siyasa domin cimma matsaya daya.
Araghchi ya bayyana haka ne a wata ganawa da ya yi a ranar Talata, da shugaban kasar Labanon, Joseph Aoun a birnin Beirut.
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya jaddada aniyar kasarsa na bunkasa alakarta da kasar Lebanon, bisa mutunta juna.
Ya kuma sanar da cewa, kamfanonin Iran a shirye suke su marawa gwamnatin Lebanon baya a kokarinta na sake gina kasar.
A nasa bangaren shugaba Aoun ya jaddada tsarin gwamnatinsa na bunkasa alaka da dukkan kasashen duniya tare da tabbatar da aniyar kasar Lebanon na kara dankon zumuncin da ke tsakaninta da Iran a fannoni daban daban.
Ya jaddada cewa kawo karshen mamayar wasu sassan kasar Lebanon da kuma gyara barnar da gwamnatin Isra’ila ta yi, su ne manyan abubuwan da sabuwar gwamnatin ta Labanon ta sa a gaba.
Araghchi ya kuma gana da firaministan kasar Lebanon Nawaf Salam, A yayin wannan ganawar, sun yi musayar ra’ayi kan bunkasuwar dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, da kuma ci gaban yankin.
Araghchi ya bayyana ziyarar tasa a matsayin wani bangare na manufofin gwamnatin Iran na karfafa alaka da kasashe makwabta da na shiyya, ciki har da Lebanon.
Kafin hakan dama ya ziyarci kasar Masar, a ci gaba da wannan manufa.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Lebanon Araghchi ya
এছাড়াও পড়ুন:
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba
Yau ce ranar muhalli ta duniya. An yi sharhi a baya cewa, a cikin ’yan shekarun nan, kasar Sin ta jagoranci ayyukan samar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba a duniya, da samun gagaruman nasarori a fannin raya makamashin da ake sabuntawa da sauran fannoni, da taimaka wa sauran kasashe masu tasowa wajen aiwatar da ayyukan sauyin makamashi.
Yayin da yake amsa tambayoyi a wurin taron manema labaru da ya gudana a yau, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya bayyana cewa, kasar Sin ta kasance mai fafutukar neman ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba a ko da yaushe, kana mai taka muhimmiyar rawa wajen kawo sauyi ta wannan fuskar a duniya, inda aka mayar da makomar dan’adam ta bai-daya.
Kasar Sin tana mai da hankali kan ba da fifiko ga kyautata muhallin halittu da samar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba, kuma tana son ci gaba da gudanar da ayyuka na bai-daya amma kuma ta bambanta hakkokin hakan tare da dukkan bangarori a matsayin “karfin da zai ba da dama” don inganta gina duniya mai tsabta, kyakkyawa da za ta zama mai dorewa. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp