Cikin kwanaki uku na hutun bikin Dragon Boat na kasar Sin, an samu karuwar tafiye-tafiye zuwa ketare da suka kusa miliyan 5.91. Masu tafiye-tafiye sun karu matuka tun daga Asabar har jiya Litinin, inda aka samu karuwar kaso 2.7 bisa dari kan adadin da aka samu a bara.

Alkaluman da hukumar lura da shige da ficen al’umma ta kasar Sin ta fitar a Talatar nan, sun nuna karuwar baki masu shigowa kasar Sin daga ketare, musamman wadanda suka ci gajiyar manufar nan ta kawar da bukatar biza.

Albarkacin wannan manufa, adadin baki daga ketare da suka shigo kasar Sin yayin ranaku uku na bikin ya kai 231,000, adadin da ya karu da kaso 59.4 bisa dari kan na shekarar bara.

A bana an gudanar da bikin Dragon Boat ne tun daga ranar Asabar 31 ga watan Mayu zuwa jiya Litinin 2 ga watan Yuni. (Mai Fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sabon Firay Ministan Sudan Ya Bukaci Kasashen Dake Taimaka Wa “RSF” Da Su Daina

Sabon fira ministan kasar Sudan Kamil Idris ya yi kira ga kasashen waje masu taimaka wa dakarun daukin gaggawa “RSF” da su kawo karshen taimakon da suke bawa masu aikata laifi.”

Idris wanda yake jawabin bayan kama aiki a jiya ya ce; Jami’an tsaro da kuma mahukuntan kasar ta Sudan suna da cikakken goyon baya a kasar don kawo karsehn ‘yan tawaye, masu dauke da makamai.”

Idris ya kuma ce; A shirye yake ya yi wa kasa aiki a cikin kekyawar anniyya da kwazo.”

Gwamantin kasar Sudan dai tana zargin Hadaddiyar Daular Larabawa da taimaka wa dakarun kai daukin gaggawa “RFS” wacce ta dauki shekaru biyu tana fafatawa da sojojin kasar.

Wasu daga cikin  kasashen da Sudan take  zargi da hannu a tawayen na “RSF” sun hada da Chadi, Libya da Sudan Ta Kudu.

Wasu rahotannin suna nuni da cewa, suna bawa wannan kungiyar makamai ne ta kan iyakokin da su ka hada wadannan kasashe da Sudan.

Tun barkewar yakin basasa a kasar Sudan a ranar 15 ga watan April 2023, zuwa yanzu adadin mutanen da su ka rasa rayukansu sun kai 24,000, yayin da wasu fiye da miliyan 14 su ka zama ‘yan gudun gijira, miliyan 4 daga cikinsu sun fice daga kasar, zuwa kasashen makwabta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Uba Sani Ya Samu Goyon Bayan Mazauna Mahuta Bayan Warware Rikicin Filaye
  • DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Kayan Miya Gabanin Bikin Sallah
  • Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 
  • Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 
  • Nasarorin Shekaru Biyun Tinubu Shaida Ne Ta Shugaba Mai Hangen Nesa – Ministan Yada Labarai
  • Ambaliyar Mokwa: Yawan mutanen da suka salwanta ya haura 700
  • Gwamnatin Yobe Ta Rufe Makarantu Na Tsawon Kwanaki 10 Don Bikin Sallah Babba
  • An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana
  • Sabon Firay Ministan Sudan Ya Bukaci Kasashen Dake Taimaka Wa “RSF” Da Su Daina