Ministan Yada Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Mohammed Idris, yace nasarorin da gwamnatin Tinubu ta samu cikin shekaru biyu kadai shaida ce ta shugabanci mai hangen nesa da jaruntaka.

 

Ya bayyana haka ne a yayin taron farko na National Dialogue on Citizen Engagement and National Security da aka gudanar a Abuja, mai taken “One Voice, One Vision: Uniting Perspectives for a Stronger Nigeria.

 

A cewar Ministan, wannan taro ya zo a daidai lokacin da Najeriya ke kokari yi amfani da damamaki da ke gabanta.

 

Ya jaddada cewa wannan dandali da Voice of Nigeria (VON) ta shirya ba kawai taron tattaunawa kan manufofi bane, sai dai wata kafa ce da aka tanada domin hada ra’ayoyi da abubuwan da talakawa ke fuskanta a rayuwarsu ta yau da kullum.

 

“Ko a makon da ya gabata,” in ji Idris, “mun yi bikin cikar gwamnatin Tinubu shekaru biyu da hujjoji masu dama na irin ci gaba da sauyi da aka samu.”

 

Ministan ya bayyana cewa babu wata gwamnati a tarihin dimokuradiyyar Najeriya da ta samu irin wadannan nasarori da sauye-sauye cikin shekaru biyu.

 

“Babu wata gwamnati da ta riga ta aiwatar da abin da gwamnatin Tinubu ta yi: Da farko, jarumtakar kawar da tallafin man fetur da magudin canjin kudi, sannan gina hanyoyi da dama, tsarin bayar da rancen karatu ga dalibai na farko a tarihin Najeriya, da kuma CreditCorp – manufofin da ke dawo da kwarin gwiwar matasa a fadin kasa.”

 

Ya kara da cewa manufofin gwamnatin Tinubu sun fara haifar da gagarumin sakamako.

 

“Duk da kalubalen farko, farashin abinci na sauka, kuma muna ci gaba da dakile matsalar rashin tsaro. Har ila yau, tasirin mulki na fara tabuka abubuwa ta hanyar: ‘yancin kan kananan hukumomi, kirkiro ma’aikatun ci gaban yankuna, da kuma babban cigaba a fannin noma – wato kafa Ma’aikatar Raya Noman Dabbobi ta Tarayya.”

 

“Ina tabbatar da cewa ƙarƙashin shugabancin Bola Ahmed Tinubu, muradun al’umma na kara hade, suna goyon bayan shugaba mai hangen nesa da jaruntaka,” in ji shi.

 

Yayin da yake fayyace muhimmancin taron, Ministan ya bayyana cewa haɗin kan ƙasa da amincewar jama’a sune ginshiƙan tsaron ƙasa.

 

“Ba za a samu tsaro ba idan ba a samu haɗin kai ba. Kuma ba za a samu haɗin kai ba idan babu amincewa. A lokacin rashin tabbas da barazana, makaminmu mafi ƙarfi ba bindiga ba ce – ita ce amincewa tsakanin masu mulki da wadanda ake mulkawa.”

 

Ya ce manufar Renewed Hope Agenda ta ginu ne akan shiga da tasirin al’umma, inda duk wani dan Najeriya ya zama mai muhimmanci, a saurare shi, a ganshi, a kuma darajanta shi.

 

Ministan ya kuma yaba da rawar da Voice of Nigeria ke takawa, inda ya ce tana kara wuce matsayin kafar yada labarai kawai.

 

“VON ba wai kawai tana watsa labarai ba ce – tana gina labari da gina matsayin kasa tana tabbatar da cewa ko da a cikin Hausa, Yarbanci, Igbo ko Turanci ne, ko a Berlin ko a Birnin Kebbi ne, muryar Najeriya na ji da daraja, kuma ana girmama ta daga cikin ƙasa daya mai haɗin kai da tsaro.”

 

Yayin da yake kiran hadin gwiwa tsakanin dukkan bangarorin kasa, Idris ya ce:

“Wannan dandalin yana nuna wannan hangen nesa – yana haɗa gwamnati, kafafen yada labarai, kungiyoyin fararen hula, da jami’an tsaro, ba cikin kangi ba, sai dai cikin hadin kai. Ba don a yi wa juna magana ba ne, sai dai a saurari juna.”

 

Ministan ya jaddada cewa Nigerians ba sai sun zama daya ba kafin su hada kai; za su iya karbar bambance bambancen juna, tare da ci gaba da zama tsintsiya madauri daya.

 

“Wannan tattaunawar ita ce misalin irin wannan dama – dandalin da ba a gogewa bambance bambance ba, sai dai a rungume su a matsayin mafita ta hadin gwiwa. Ina kira gare mu da mu fita daga nan ba da tunani kawai ba – sai dai da niyyar aiki. Sabuwar niyya ga gaskiya a kafafenmu, adalci a manufofinmu, gaskiya a mulkinmu, da jin kai a cikin al’ummarmu.”

 

Wadanda suka halarci taron sun hada da Ministan Harkokin Jin Kai da Rage Talauci, Farfesa Nentawe Goshe Yilwatda; Babban Hafsan Tsaro, Janar Christopher Musa; Shugaban Hukumar Kiyaye Hadurran Hanya (FRSC), Shehu Mohammed; Daraktan Hukumar Kula da Jaridu, Dr. Dili Ezugha; Daraktan Hukumar Wayar da Kan Jama’a, Malam Lanre Issa-Onilu; Shugaban Hukumar Masana Yada Labarai (NIPR), Dr. Ike Neliaku; Tsohon Babban Hafsan Sojojin Kasa, Janar Yusuf Tukur Buratai; da Babban Sakatare na Ma’aikatar Yada Labarai da Wayar da Kan Jama’a ta Tarayya, Mista Ogbodo Chinasa Nnam, da sauransu.

 

Adamu Yusuf

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Labarai Nasarorin Shekaru Yada

এছাড়াও পড়ুন:

Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi

Hukumomin a Ƙasar Saudiyya, sun saki wasu ’yan Najeriya uku da aka kama a Jeddah kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi.

Waɗanda aka saki sun haɗa da Hajiya Maryam Hussain Abdullahi, Hajiya Abdullahi Bahijja Aminu, da Malam Abdulhamid Saddieq.

Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano

Sun shafe makonni huɗu a tsare kafin aka tabbatar da cewa ba su da laifi.

A wajen taron manema labarai a Abuja, mai magana da yawun Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi (NDLEA), Femi Babafemi, ya ce sakin ya biyo bayan tttaunawa da Shugaban NDLEA, Janar Mohamed Buba Marwa (mai ritaya), tare da Hukumar Hana Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Saudiyya.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ne, ya bayar da cikakken goyon baya wajen ganin an saki waɗanda aka kama.

Bincike ya gano cewa wasu masu safarar miyagun ƙwayoyi ne a Filin Jirgin Sama na Mallam Aminu Kano, suka ƙwayoyin a jakunkuna waɗanda aka kama.

Mutanen uku da aka kama, sun tashi a jirgin Ethiopian Airlines a ranar 6 ga watan Agusta don yin Umara, amma aka kama su a Saudiyya.

Binciken NDLEA ya kai ga kama wani shugaban masu safarar miyagun ƙwayoyin, mai shekaru 55, Mohammed Ali Abubakar (wanda aka fi sani da Bello Karama).

Hakazalika, hukumar ta kama wasu mutum uku ciki har da ma’aikatan jirgi.

Mutanen da aka kama su ne suka shirya safarar ƙwayoyin a jakunkunan mutane da aka kama a Saudiyya.

NDLEA ta gabatar da shaidun da suka tabbatar da cewa mutanen da aka kama a Saudiyya ba su da laifi.

Sakamakon haka, hukumomin Saudiyya suka sako ɗaya daga cikinsu a ranar 14 ga watan Satumba, sannan suka sako sauran biyun a ranar 15 ga watan Satumba.

Babafemi, ya ce Marwa ya gode wa hukumomin Saudiyya saboda mutunta yarjejeniyar haɗin kai tsakaninsu da Najeriya.

Ya kuma gode wa Shugaba Tinubu da sauran manyan jami’an gwamnati, ciki har da Ministan Shari’a, Ministan Harkokin Ƙasashen Waje, Ministan Sufurin Jiragen Sama, da Mai Bai Wa Shugaba Shawara Kan Harkar Tsaro, saboda gudummuwarsu.

Ya ƙara da cewa wannan lamari ya nuna cewa Najeriya tana tsayawa wajen kare ‘yan ƙasarta a ƙasashen waje kuma ba za ta yadda wani ɗan Najeriya ya sha wahala saboda laifin da bai aikata ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 
  • Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
  • Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBS
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta
  • Sarki Sanusi II ya koka kan yawan cin bashin Najeriya
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa