Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya jaddada cewa: Tsibiran guda uku na Tunb Babba da Tunb Karami da Abu Musa yankuna ne Iran

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya yi watsi da ikirari da kungiyar hadin kan kasashen Larabawan yankin tekun Fasha (PGCC) ta yi dangane da tsibiran Iran guda uku, yana mai jaddada cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta dauki dukkan matakan da suka dace don tabbatar da tsaro da muradun kasar a cikin tsibiran guda uku.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Iran ya jaddada matsayin Jamhuriyar Musulunci ta Iran tare da yin watsi da ikirarin da ke kunshe a cikin bayanin karshe na taron ministocin harkokin wajen kasashen yankin tekun Fasha karo na 64 dangane da tsibiran kasar Iran guda uku na Tunb Babba, Tunb Karami da Abu Musa.

Baqa’i ya yi watsi da zarge-zargen da ke kunshe cikin wannan bayani dangane da hukunci da matakan shari’a da hukumomin Iran da abin ya shafa suka dauka dangane da tsibiran da aka ambata, yana mai cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta dauki duk wani matakin da ya dace don tabbatar da tsaro da muradun kasar a cikin tsibiran guda uku, da suka hada da filayenta, ruwa, da sararin samaniyarta, daidai da hakkinta na ‘yancin kai.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: harkokin wajen Iran guda uku

এছাড়াও পড়ুন:

Fizishkiyan: Batun Kare Hakkin Bil’adama Ba Komai Ba Ne Sai Karya

Shugaban kasar Iran Mas’ud Fizishkiyan ya bayyana cewa; Batun kare hakkin bil’adama da ake yi a duniya ba komai ba ne sai karya.

Shugaba Fizishkiyan ya yi ishara da yadda masu ikirarin kare hakkin bil’adama suke sa kafafunsu suna take hakkin mutanen Gaza da cikin kasashen yammacin Asiya da kuma tafka manyan laifuka.

A yau Talata ne dai shugaban kasar ta Iran ya gabatar da jawabi a wurin bikin girmama shahidan kallafaffen yaki na kwanaki 12, ya bayyana cewa: “A cikin wannan duniyar wacce take riya ci gaba da wayewa, a gaba idon duniya, ake yanke wa mutanen Gaza ruwan sha da abinci, a hana mata da kananan yara. Haka nan kuma ake tafka laifukan da su ka kunshi kisan kiyashi, amma kuma wai su ne ke Magana akan kare hakkin bil’adama.”

Shugaban kasar ta Iran ya kuma ce, masu yin Magana akan kare hakkin bil’adama din ne suke sa kafafunsu suna take shi.

Shugaban kasar ta Iran ya kuma ce, HKI da Amurka, sun kawo hari bisa riya cewa Iran tana son kera makamin Nukiliya, kuma wadanda su ka kai wa harin mata ne, kananan yara da kuma sauraren hula da ba su da makamai.

Shugaban kasar ta Iran ya ambato hudubar da Imam Hussain ( a.s) ya yi wa abokan gabarsa a karbala cewa: “Idan ba ku da addini, to ku zama ‘yantattun a cikin harkokinku na duniyu.”

Shugaba Fizishkiyan ya kara da cewa: A wannan lokacin suna yanke abinici da ruwa ga mutanen Gaza, sannan kuma a lokaci daya suna Magana akan kare hakkin bil’adama. Wane annabi ko addinin Allah ne ya halarta tafka laifuka irin wannan ?

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Yi Mu’amala Da Kasashen Dake Kan Karshen Kogin Yarlung Zangbo Dangane Da Batun Gina Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Karfin Ruwa A Kogin
  •  Iraki Ta Yi Watsi Da Bukatar Amurka Akan Dakarun Sa Kai Na” Hashdus-sha’abi”
  • Jami’an Kasashen Rasha, China, Iran Sun Gudanar Da Taron Hadin Gwiwa A Tehran
  • Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar
  • Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu
  •  Kungiyar Malaman Musulmi Ta Yi Fatawar Wajabcin Kawo Karshen Killace Gaza
  • Fizishkiyan: Batun Kare Hakkin Bil’adama Ba Komai Ba Ne Sai Karya
  • Kasar Sin Na Fatan EU Za Ta Yi Aiki Da Ita Bisa Alkibla Guda Da Tsara Hadin Gwiwa Na Shekaru 50 Masu Zuwa
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce; Iran Ba Zata Bar Tace Sinadarin Uranium Ba
  • Ministocin Tsaron kasashen Rasha Da JMI Sun Hadu A Birnin Mosco