Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi wanda yake ziyar aiki a kasar Lebanon bayyana cewa kasarsa tana goyon bayan hadin kan mutanen kasar Lebanon.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadar haka bayan ganawarsa da shugaban majalisar dokokin kasar ta Lebanon a yau Talata a birnin Beirut babban birnin kasar.

Aragchi ya ce kasar Iran tana goyon bayan kasar Lebanon ta hanyar kungiyar Hizbullah. Kuma tana goyon bayanta kan HKI wacce take mamaye da wasu yankuna a kasar. Muna goyon bayan gwamnati da mutane a duk wani kokarin da zasu yi na kwato yankunan kasar wadanda HKI take mamaye da su.

 Ministan kafin haka ya bayyana cewa JMI tana daga cikin kasashen da zasu taimakawa kasar Lebanon ta sake gina wuraren da HKI ta lalata a yankin shekarar da ta gabata. Kuma muna goyon bayan tattaunawa tsakanin yan kasa.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: tana goyon bayan kasar Lebanon

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Sin Na Fatan EU Za Ta Yi Aiki Da Ita Bisa Alkibla Guda Da Tsara Hadin Gwiwa Na Shekaru 50 Masu Zuwa

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun, ya bayyana a yayin gudanar da taron manema labaru na yau da kullum da aka yi yau Litinin cewa, bana shekara ce ta cika shekaru 50 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da Tarayyar Turai EU. Kuma taron kolin kasar Sin da EU karo na 25 na karatowa. Kasar ta Sin tana fatan kungiyar EU za ta yi aiki tare da ita bisa alkibla guda, da cimma matsaya, da kawar da bambance-bambance, da kuma tsara shirin hadin gwiwa tare cikin shekaru 50 masu zuwa.

Bayan cimma yarjejeniya tsakanin Sin da kungiyar EU, shugaban majalisar Tarayyar Turai António Costa da shugabar hukumar Tarayyar Turai Ursula von der Leyen, za su ziyarci kasar Sin a ranar 24 ga watan Yuli. Shugaban kasar Sin Xi Jinping zai gana da shugabannin na EU guda biyu. Kazalika, firaministan kasar Sin Li Qiang, zai jagoranci taron koli na Sin da EU karo na 25 tare da shugabannin kungiyar ta EU guda biyu.

Bugu da kari, wasu jami’an diflomasiyyar Turai sun bayyana cewa, kasar Sin na kokarin yin amfani da damar sake fasalin hukumomi don bikin cika shekaru 80 da kafuwar MDD wajen fadada tasirinta a MDD. A yayin da yake mayar da martani kan wannan batu, Guo Jiakun ya ce, kasar Sin na son yin hadin gwiwa tare da kasashen Turai wajen daukar bikin cika shekaru 80 da kafuwar MDD a matsayin wata dama ta kara karfafa muhimmin matsayin da MDD take da shi, da taka rawar da ta dace a matsayinta na MDD yadda ya kamata, da sanya kwarin gwiwa da karfafa damawa da bangarori daban daban. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kama Wata Mata Da Take Shirin Kashe Benjemin Netanyahu
  • Jami’an Kasashen Rasha, China, Iran Sun Gudanar Da Taron Hadin Gwiwa A Tehran
  • Eritrea ta gargadi Habasha game da yunkurin kafa tashar jiragen ruwa a cikin yankinta
  • Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar
  • Kasar Sin Tana Da Dokoki Da Ka’idoji Sama Da 180 Dake Kare Nakasassu
  • Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu
  • Mutum 16 sun mutu a haɗarin jirgin sama a Bangladesh
  • Kasar Sin Na Fatan EU Za Ta Yi Aiki Da Ita Bisa Alkibla Guda Da Tsara Hadin Gwiwa Na Shekaru 50 Masu Zuwa
  • Gwamna Radda Da Makarrabansa Na Samun Kulawa A Asibiti Bayan Hatsarin Mota A Hanyar Daura
  • Ministocin Tsaron kasashen Rasha Da JMI Sun Hadu A Birnin Mosco