Aragchi: Iran Tana Goyon Bayan Tattaunawa Saboda Hadin Kai Tsakanin Mutanen Lebanon
Published: 3rd, June 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi wanda yake ziyar aiki a kasar Lebanon bayyana cewa kasarsa tana goyon bayan hadin kan mutanen kasar Lebanon.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadar haka bayan ganawarsa da shugaban majalisar dokokin kasar ta Lebanon a yau Talata a birnin Beirut babban birnin kasar.
Aragchi ya ce kasar Iran tana goyon bayan kasar Lebanon ta hanyar kungiyar Hizbullah. Kuma tana goyon bayanta kan HKI wacce take mamaye da wasu yankuna a kasar. Muna goyon bayan gwamnati da mutane a duk wani kokarin da zasu yi na kwato yankunan kasar wadanda HKI take mamaye da su.
Ministan kafin haka ya bayyana cewa JMI tana daga cikin kasashen da zasu taimakawa kasar Lebanon ta sake gina wuraren da HKI ta lalata a yankin shekarar da ta gabata. Kuma muna goyon bayan tattaunawa tsakanin yan kasa.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: tana goyon bayan kasar Lebanon
এছাড়াও পড়ুন:
Araghchi : Babu wata tattaunawa idan ba zamu tace uranium ba
Babban jami’in diflomasiyyar Iran ya sake tabbatar da cewa Iran ba za ta taba yin kasa a gwiwa ba kan ‘yancinta na tace Uranium, yana mai cewa ci gaban da kasar ta samu a fannin makamashin nukiliya ya samo asali ne sakamakon sadaukarwa da kuma saka hannun jari na kasa.
A cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na X, ministan harkokin wajen kasar Abbas Araghchi ya ce, ba batun inganta makamashin Uranium a duk wata yarjejeniyar nukiliya da za a yi nan gaba.
“Iran ta saka kudi da yawa domin kai wag a wannan mataki, sannan kuma ba zai sa mu yi watsi da sadaukarwar da ‘yan kishin kasa sukayi don tabbatar da burinmu.
Araghchi ya bayyana tace uranium a matsayin wani sakamako na ilimi da fasaha, mahimman abubuwan da suka ba Tehran damar habaka fasahar nukiliya cikin lumana duk da takunkumin shekaru da matsin lamba na kasa da kasa.
Yayin da yake bayyana matsayin Iran a tattaunawar da Amurka, ya kara da cewa: “Babu wata yarjejeniya idan ba zamu tace uranium ba, amma zamu iya cimma yarjejeniya wacce ta tanadi hana mallakar makamin nukiliya.”
Ya zuwa yanzu dai Iran da Amurka sun gudanar da jerin tattaunawa har sau biyar da nufin maye gurbin yarjejeniyar nukiliyar da aka cimma a shekarar 2015.