Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Alakar Iran Da Lebanon Tarihi Ce Mai Tushe Da Ta Ginu Kan Mutunta Juna
Published: 3rd, June 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa; Dangantakar Iran da Lebanon tarihi ce, mai tushe, kuma ta ginu ne bisa mutunta juna
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya bayyana alakar da ke tsakaninta da kasar Lebanon a matsayin mai tarihi, mai tushe, kuma ta ginu ce bisa mutunta juna. Ya ce: “Kasashen biyu sun kuduri aniyar bunkasa wannan alakar.
A jawabin da ya yi a filin jirgin sama na birnin Beirut, inda wakilin kakakin majalisar dokokin kasar Lebanon ya tarbe shi, Araqchi ya yi nuni da cewa ziyarar wani bangare ne na rangadin da yake yi a yankin bayan ziyarar da ya kai birnin Alkahira na Masar, kuma zai gana da jami’an kasar ta Lebanon.
Ya kara da cewa, alakar Iran da Lebanon ta kasance mai tarihi, mai tushe, kuma ta ginu ce bisa mutunta juna, sannan Iran ta kuduri aniyar raya wannan alakar. Ya kara da cewa, Suna ba wa ‘yantacciyar kasar Lebanon matukar muhimmanci da kuma ba da goyon bayansu wajen tunkarar ‘yan mamaya.
Ministan harkokin wajen na Iran ya ci gaba da cewa: A ko da yaushe suna goyon bayan ‘yancin kan kasar Lebanon a kowane mataki, kuma suna ci gaba da ba ta goyon baya a cikin mawuyacin halin da ake ciki.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Lebanon
এছাড়াও পড়ুন:
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
Babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin CMG, ya gabatar da labarin ganawar da aka yi jiya Alhamis tsakanin shugabannin Sin da Amurka a Busan na Korea ta Kudu, cikin harsuna 85. Kuma zuwa yau Juma’a, mutanen da suka karanta rahotanni masu alaka da ganawar ta hanyoyin watsa labarai na dandalin CMG sun kai miliyan 712. Haka kuma, kafafen watsa labarai na kasa da kasa 1678, sun wallafa tare da tura rahotanni da bidiyon labaran CMG na harsuna daban daban game da ganawar, har sau 4431.
Har ila yau a wannan rana, an gudanar taron tattaunawa na kasa da kasa kan bude kofa da kirkire kirkire da ci gaba na bai daya a kasar Uruguay, wanda CMG da hadin gwiwar ofishin jakadancin Sin dake kasar suka shirya a Montevideo babban birnin Uruguay. (Mai fassara: FMM)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA