Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Alakar Iran Da Lebanon Tarihi Ce Mai Tushe Da Ta Ginu Kan Mutunta Juna
Published: 3rd, June 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa; Dangantakar Iran da Lebanon tarihi ce, mai tushe, kuma ta ginu ne bisa mutunta juna
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya bayyana alakar da ke tsakaninta da kasar Lebanon a matsayin mai tarihi, mai tushe, kuma ta ginu ce bisa mutunta juna. Ya ce: “Kasashen biyu sun kuduri aniyar bunkasa wannan alakar.
A jawabin da ya yi a filin jirgin sama na birnin Beirut, inda wakilin kakakin majalisar dokokin kasar Lebanon ya tarbe shi, Araqchi ya yi nuni da cewa ziyarar wani bangare ne na rangadin da yake yi a yankin bayan ziyarar da ya kai birnin Alkahira na Masar, kuma zai gana da jami’an kasar ta Lebanon.
Ya kara da cewa, alakar Iran da Lebanon ta kasance mai tarihi, mai tushe, kuma ta ginu ce bisa mutunta juna, sannan Iran ta kuduri aniyar raya wannan alakar. Ya kara da cewa, Suna ba wa ‘yantacciyar kasar Lebanon matukar muhimmanci da kuma ba da goyon bayansu wajen tunkarar ‘yan mamaya.
Ministan harkokin wajen na Iran ya ci gaba da cewa: A ko da yaushe suna goyon bayan ‘yancin kan kasar Lebanon a kowane mataki, kuma suna ci gaba da ba ta goyon baya a cikin mawuyacin halin da ake ciki.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Lebanon
এছাড়াও পড়ুন:
Aragchi: Iran Tana Goyon Bayan Tattaunawa Saboda Hadin Kai Tsakanin Mutanen Lebanon
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi wanda yake ziyar aiki a kasar Lebanon bayyana cewa kasarsa tana goyon bayan hadin kan mutanen kasar Lebanon.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadar haka bayan ganawarsa da shugaban majalisar dokokin kasar ta Lebanon a yau Talata a birnin Beirut babban birnin kasar.
Aragchi ya ce kasar Iran tana goyon bayan kasar Lebanon ta hanyar kungiyar Hizbullah. Kuma tana goyon bayanta kan HKI wacce take mamaye da wasu yankuna a kasar. Muna goyon bayan gwamnati da mutane a duk wani kokarin da zasu yi na kwato yankunan kasar wadanda HKI take mamaye da su.
Ministan kafin haka ya bayyana cewa JMI tana daga cikin kasashen da zasu taimakawa kasar Lebanon ta sake gina wuraren da HKI ta lalata a yankin shekarar da ta gabata. Kuma muna goyon bayan tattaunawa tsakanin yan kasa.