Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa; Dangantakar Iran da Lebanon tarihi ce, mai tushe, kuma ta ginu ne bisa mutunta juna

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya bayyana alakar da ke tsakaninta da kasar Lebanon a matsayin mai tarihi, mai tushe, kuma ta ginu ce bisa mutunta juna. Ya ce: “Kasashen biyu sun kuduri aniyar bunkasa wannan alakar.

A jawabin da ya yi a filin jirgin sama na birnin Beirut, inda wakilin kakakin majalisar dokokin kasar Lebanon ya tarbe shi, Araqchi ya yi nuni da cewa ziyarar wani bangare ne na rangadin da yake yi a yankin bayan ziyarar da ya kai birnin Alkahira na Masar, kuma zai gana da jami’an kasar ta Lebanon.

Ya kara da cewa, alakar Iran da Lebanon ta kasance mai tarihi, mai tushe, kuma ta ginu ce bisa mutunta juna, sannan Iran ta kuduri aniyar raya wannan alakar. Ya kara da cewa, Suna ba wa ‘yantacciyar kasar Lebanon matukar muhimmanci da kuma ba da goyon bayansu wajen tunkarar ‘yan mamaya.

Ministan harkokin wajen na Iran ya ci gaba da cewa: A ko da yaushe suna goyon bayan ‘yancin kan kasar Lebanon a kowane mataki, kuma suna ci gaba da ba ta goyon baya a cikin mawuyacin halin da ake ciki.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Lebanon

এছাড়াও পড়ুন:

Pezeshkian: Tunanin Kawo Karshen Shirin Nukiliyar Iran Ya Yi Kama Da Tabuwa

Shugaba Masoud Pezeshkian ya yi watsi da hankoron Amurka na tunzura kawayenta, musamman gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila, na yunkurin kawo karshen shirin nukiliyar Iran.

Shugaban an Iran ya bayyana hakan ne yayin wata hira da gidan talabijin na Aljazeera na kasar Qatar a wannan  Talata, inda ya bayyana cewa, za a ci gaba da inganta sinadarin Uranium a kasar Iran nan gaba bisa tsarin dokokin kasa da kasa.

Wannan yunkuri yasa an ga bangarorin biyu na Amurka da Isra’ila suna matsa lamba a kan sauran bangarori na duniya, tare da bayyana Shirin na Iran a matsayin mai matukar hadari ga duniya, da nufin samun goyon bayan kasashen duniya kan bakaken manufofisu a kan kasar ta Iran.

Dangane da zargin da shugaban Amurka Donald Trump ya yi kan Shirin Iran da kuma neman samoma kansa hujjoji na kaiwa Iran hari, da kuma bayyana cewa harin Amurka ya kawo karshen Shirin Iran na nukiliya, Pezeshkian ya ce, “Da’awar cewa shirinmu na nukiliya ya kawo karshe, batu ne na yaudara.”

“Ilimin nukiliya yana a cikin kwakwalen masananmu ne na kimiyyarmu, ba a cikin wurarenmu ba.” In ji Pezeshkian.

Haka nan kuma shugaban na Iran ya sake nanata matakin kin amincewa da zargin kasarsa da hakoron kera makaman kare dangi, da kuma kara jaddada matsayin kasar na ci gaba da daukar matakan da take yi wajen kara inganta shirinta na makamashin nukiliya domin ayyukan farar hula.

Pezeshkian ya kuma sake nanata shirye-shiryen Iran na yin shawarwarin da ba su ginu a kan haramtawa Iran hakkinta na inganta na tace sanadarin Uranium ba, amma ya ce “duk wata tattaunawa da za a yi a nan gaba dole ne ta dogara a kan batutuwa na masu tabbatar da hakkokin Iran.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Iraki Ta Yi Watsi Da Bukatar Amurka Akan Dakarun Sa Kai Na” Hashdus-sha’abi”
  • Tinubu na amfani da ƙarfin mulki wajen tsoratar da ’yan adawa — Sule Lamido
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Jaddada Hakkinta Na Tace Sinadarin Uranium A Cikin Kasarta
  • Pezeshkian: Tunanin Kawo Karshen Shirin Nukiliyar Iran Ya Yi Kama Da Tabuwa
  • Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar
  • Majalisar Dattawa ta sahale wa Tinubu karɓo rancen $21bn a ƙetare
  • Fizishkiyan: Batun Kare Hakkin Bil’adama Ba Komai Ba Ne Sai Karya
  • Kasar Sin Na Fatan EU Za Ta Yi Aiki Da Ita Bisa Alkibla Guda Da Tsara Hadin Gwiwa Na Shekaru 50 Masu Zuwa
  • Hukumar Kashe Gobara Ta Jihar Kwara Ta Taimaka Wajen Hana Lalacewar Wani Bene A Ilorin
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce; Iran Ba Zata Bar Tace Sinadarin Uranium Ba