Turkiya: Akwai Fatan Yiyuwar A Dakatar Da Yaki Tsakanin Rasha Da Ukiraniya
Published: 3rd, June 2025 GMT
Ofishin shugaban kasar Turkiya, ya bayyana fatan cewa tattaunawar da ake yi a tsakanin Rasha da Ukiraniya a birnin Istanbul, za ta kai ga tsayar da tsagaita budewa juna wuta wanda kuma zai ga, kawo karshen yakin baki daya.
Ofishin shugaban kasar Turkiya ya bayyana haka a yau Talata, ta kuma kara da cewa,; Tattaunawar da aka gudanar a jiya Litinin a tsakanin Rasha da Ukiraniya a kuma fadar shugaban kasar Turkiyya dake birnin Istanbul tana cike da fata na tsayar da yakin.
Kamfanin dilalncin labarun “Sputnik” na kasar rasha ya ambato majiyar fadar shugaban kasar ta Turkiya tana cewa; Shakka babu duk wata tattaunawa da bangarori za su zauna akan teburi, tana tattare da kyakkyawan fata, a dalilin haka, da akwai kyakkyawar fatan kai wa ga daina yaki.
Dama dai tun a jiya Litinin ne ministan harkokin wajen Turkiya, Hakan Fidan ya yi fatan ganin tattaunawar ta kai ga sakamakon da ake nema a cikin kankanen lokaci.
A nashi bangaren, jagoran tawagar Rasha a wajen tattaunawar Vladimir Medinsky ya fada wa taron manema labaru kan cewa; Rasha ta gabatar da tata mahangar a kan yadda take ganin ya kamata a kawo karshen yakin.”
Haka nan kuma ya ce, sun gabatarwa da Turkiya mahangar mai bangarori biyu, ta farko ita ce, yadda za a shimfida zaman lafiya maidorewa, ta biyu kuma kan yadda za a tsayar da wutar yaki.”
An fara bude tattaunawa tsakanin Rasha da Ukiraniya ne, a ranar 16 ga watan Mayun da ya gabata, wanda ya kai ga cimma matsaya a kan wasu batutuwa da su ka hada da musayar fursunoni.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Rasha da Ukiraniya shugaban kasar
এছাড়াও পড়ুন:
Kasar Sin: Amurka Ta Yi Matukar Kawo Cikas Ga Yarjejeniyar Da Aka Cimma A Tattaunawar Geneva
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp