HausaTv:
2025-06-05@11:52:27 GMT

Turkiya: Akwai Fatan Yiyuwar A Dakatar Da Yaki Tsakanin Rasha Da Ukiraniya

Published: 3rd, June 2025 GMT

Ofishin shugaban kasar Turkiya, ya bayyana fatan cewa tattaunawar da ake yi a tsakanin Rasha da Ukiraniya a birnin Istanbul, za ta kai ga tsayar da tsagaita budewa juna wuta wanda kuma zai ga, kawo karshen yakin baki daya.

Ofishin shugaban kasar Turkiya ya bayyana haka a yau Talata, ta kuma kara da  cewa,; Tattaunawar da aka gudanar a jiya Litinin a tsakanin Rasha da Ukiraniya a kuma fadar shugaban kasar Turkiyya dake birnin Istanbul tana cike da fata na tsayar da yakin.

Kamfanin dilalncin labarun “Sputnik” na kasar rasha ya ambato majiyar fadar shugaban kasar ta Turkiya tana cewa; Shakka babu duk wata tattaunawa da bangarori za su zauna akan teburi, tana tattare da kyakkyawan fata, a dalilin haka, da akwai kyakkyawar fatan kai wa ga daina yaki.

Dama dai tun a jiya Litinin ne ministan harkokin wajen Turkiya, Hakan Fidan ya yi fatan ganin tattaunawar ta kai ga sakamakon da ake nema a cikin kankanen lokaci.

A nashi bangaren, jagoran tawagar Rasha a wajen tattaunawar Vladimir Medinsky ya fada wa taron manema labaru kan cewa; Rasha ta gabatar da tata mahangar a kan yadda take ganin ya kamata a kawo karshen yakin.”

Haka nan kuma ya ce, sun gabatarwa da Turkiya mahangar mai bangarori biyu, ta farko ita ce, yadda za a shimfida zaman lafiya maidorewa, ta biyu kuma kan yadda za a tsayar da wutar yaki.”

An fara bude tattaunawa tsakanin Rasha da Ukiraniya ne, a ranar 16 ga watan Mayun da ya gabata, wanda ya kai ga cimma matsaya a kan wasu batutuwa da su ka hada da musayar fursunoni.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Rasha da Ukiraniya shugaban kasar

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Sin: Amurka Ta Yi Matukar Kawo Cikas Ga Yarjejeniyar Da Aka Cimma A Tattaunawar Geneva

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa
  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Cewa: Amurka Da Isra’ila Suna Da Mugun Nufi Kan Iran Da Kasashen Musulmi
  • Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva
  • Tsohon Jami’in Gwamnatin Biden Na Amurka Ya Tabbatar Da Cewa Isra’ila Ta Tafka Laifukan Yaki
  • Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus
  • Rikici Yana Ci Gaba Da Gudanar A Kasar Sudan Tsakanin Sojoji Da Dakarun Kai Daukin Gaggawa
  • Kasar Sin: Amurka Ta Yi Matukar Kawo Cikas Ga Yarjejeniyar Da Aka Cimma A Tattaunawar Geneva
  • Arakci: Cinikayya A Tsakanin Iran Da Masar Za Ta Kara Bunkasa
  • Turkiya: An Bude Tattaunawa A Tsakanin Rasha Da Ukiraniya