Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet
Published: 3rd, June 2025 GMT
Hukumar ta buƙaci jama’a da su kasance cikin shiri tare da bibiyar sabbin rahotannin yanayi da ta ke fitarwa.
Ta kuma ja hankalin hukumomin da ke kula da madatsun ruwa da su saka ido kan matakin ruwa domin gujewa cike-ciken da ka iya haddasa ambaliya.
Rahoton ya ƙara da cewa jihohin kudancin Nijeriya da kuma na Arewa ta Tsakiya za su riƙa samun ruwan sama da iska a kai a kai.
Sai dai NiMet ta ce jihohin Kwara, Kogi, Neja, Nasarawa, Benuwe, Taraba, Adamawa, Kaduna, Kano, Katsina, Sakkwato, Edo, Delta da Abuja ba za su samu ruwan sama da yawa kamar yadda aka saba ba.
Hukumar ta buƙaci manoma da su yi amfani da dabarun zamani da ilimin kimiyya wajen gudanar da harkokin noma a wannan daminar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Ambaliyar Ruwa
এছাড়াও পড়ুন:
Kasa ta danne almajirai 11 sun mutu a Kaduna
Wasu almajirai su 11 sun rasa rayukansu bayan kasa ta danne su a kauyen ’Yardoka da ke karamar hukumar Kubau ta jihar Kaduna.
Bayanai sun nuna almajiran sun rasu ne lokacin da suke tsaka da hakar kasa domin taya malaminsu buga bulon kasa da zai yi gini da shi.
Lamarin ya faru ne wajen misalign karfe 1:45 na ranar Litinin.
’Yan sanda sun sake hana hawan Sallah a Kano Ambaliyar Mokwa: Yawan mutanen da suka salwanta ya haura 700Almajiran dai da aka bayyana rasuwar tasu sun hada da Muntari Abdulkadir da Aliyu Abba da Ali Umar da Mubarak Haruna da Usain Isa da Yusuf Shafiu da Mujitafa Jibril da Yusha’u Saidu da Aliyu Abdu da Hamisu Mohammed da kuma Ali Abdulmumini, dukkansu ’yan shekaru 10 zuwa 15 ne.
Wasu daga cikinsu dai ’yan garin da lamarin ya faru ne, yayin da wasu daga ciki suka fito daga makwabtan garin a yankin Damau.
Kazalika, an samu nasarar ceto wasu mutum bakwai da raunuka a jikinsu, inda aka garzaya da su asibitin garin inda yanzu haka suke can suna samun kulawar ma’aikatan lafiya.
Rundunar ’Yan Sanda ta jihar Kaduna ta tabbatar da faruwar lamarin ta bakin kakakinta a jihar, DSP Mansir Hassan.
Kakakin ya ce jim kadan da samun rahoton faruwar lamarin ne suka aike da jami’ansu wajen bayan sun samu kiran gaggawa.
Ya kuma ce tuni suka kaddamar da bincike domin gano musabbabin faruwar lamarin.