Ministan harkokin wajen Iran ya soki rahoton hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya yayin ganawa da Grossi a birnin Alkahira

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya soki sabon rahoton da hukumar ta IAEA ta fitar kan shirin makamashin nukiliyar kasar Iran yayin ganawarsa da babban darektan hukumar ta makamashin nukiliya ta duniya Rafa’el Grossi a birnin Alkahira.

A yayin taron, wanda aka gudanar a babban birnin Masar bisa bukatar Grossi, Araqchi ya tunatar da hukumar ta IAEA da babban daraktan ta game da alhakin da ya rataya a wuyansu na gudanar da ayyukansu cikin kwarewa.

Har ila yau ministan harkokin wajen na Iran ya soki zarge-zarge marasa tushe da ke kunshe cikin sabon rahoton hukumar ta IAEA kan shirin nukiliyar Iran na zaman lafiya tare da jaddada cewa bai kamata hukumar ta IAEA ta amince mai tasirantuwa da matsin lamba na siyasa da kuma manufar wasu kasashe mambobin kungiyar ba.

Bayan ganawar, Grossi ya wallafa wani rubutu a shafinsa na Twitter, inda ya bayyana ganawarsa da ministan harkokin wajen Iran Seyyed Abbas Araqchi, wanda yake ziyara a birnin Alkahira, a gaban ministan harkokin wajen Masar Badr Abdel Aty.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: hukumar ta IAEA harkokin wajen

এছাড়াও পড়ুন:

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

Yanzu haka an shiga shekaru 10 na zagaye na 2 na karni na 21, kuma duniya na fuskantar kwaskwarima, da sauye-sauyen da ba a taba ganin irinsu ba a tarihi, wanda ya zarce tunanin da ake yi.

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana kwaskwarimar da ake fuskanta a matsayin “Babban sauyi da ba a taba ganin irinsa ba cikin karni daya”, wanda ya hada da kyautatuwar karfi tsakanin mabambantan kasashe da ya zarce zaton da aka yi a baya, matakin ya tabbatar da alkiblar da Sin za ta bi, har ma ya kunshi sauye-sauyen al’adu da wayewar kan Bil Adama.

Yau za mu ganin ma’anar maganar Xi Jinping kan wannan batu dake jawo hankalinmu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 
  • Sheikh Naim Qassem Da Aragchi Sun Tabbatar Da Kara Karfin Zumunci Tsakanin Iran Da Lebanon
  • Iran Ta Jaddada Hakkinta Na Mayar Da Martani Kan Bakar Siyasar Kwamitin Gwamnonin Hukumar IAEA
  • Sin Da Masar Sun Cimma Yarjejeniyar Kafa Cibiyar Harkokin Kasuwanci Ta Sabon Birnin Masar 
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Alakar Iran Da Lebanon Tarihi Ce Mai Tushe Da Ta Ginu Kan Mutunta Juna
  • Iran Ta Yi Watsi Da Da’awar Kungiyar Hadin Kan Kasashen Larabawa Na Da’awar Mallakar Wasu Yankunan Iran
  • Arakci: Cinikayya A Tsakanin Iran Da Masar Za Ta Kara Bunkasa
  • Kasar Iran Ta Soki Rahoton Hukumar IAEA Na Baya-Bayan Nan Shirinta Na Makamashin Nukiliya
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Yana Ziyarar Aiki A Kasar Masar, inda Ya Gana Da Shugaban Kasar