Ministan harkokin wajen Iran ya soki rahoton hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya yayin ganawa da Grossi a birnin Alkahira

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya soki sabon rahoton da hukumar ta IAEA ta fitar kan shirin makamashin nukiliyar kasar Iran yayin ganawarsa da babban darektan hukumar ta makamashin nukiliya ta duniya Rafa’el Grossi a birnin Alkahira.

A yayin taron, wanda aka gudanar a babban birnin Masar bisa bukatar Grossi, Araqchi ya tunatar da hukumar ta IAEA da babban daraktan ta game da alhakin da ya rataya a wuyansu na gudanar da ayyukansu cikin kwarewa.

Har ila yau ministan harkokin wajen na Iran ya soki zarge-zarge marasa tushe da ke kunshe cikin sabon rahoton hukumar ta IAEA kan shirin nukiliyar Iran na zaman lafiya tare da jaddada cewa bai kamata hukumar ta IAEA ta amince mai tasirantuwa da matsin lamba na siyasa da kuma manufar wasu kasashe mambobin kungiyar ba.

Bayan ganawar, Grossi ya wallafa wani rubutu a shafinsa na Twitter, inda ya bayyana ganawarsa da ministan harkokin wajen Iran Seyyed Abbas Araqchi, wanda yake ziyara a birnin Alkahira, a gaban ministan harkokin wajen Masar Badr Abdel Aty.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: hukumar ta IAEA harkokin wajen

এছাড়াও পড়ুন:

Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Jaddada Hakkinta Na Tace Sinadarin Uranium A Cikin Kasarta

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa; Ba zai yiwu Iran ta iya yin watsi da shirinta na inganta sinadarin Uranium ba

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa: Har yanzu ba a daina sarrafa sinadarin Uranium ba a Iran, duk da irin barnar da hare-haren Amurka ya yi wa cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran.

A wata hirarsa da Fox News, Araqchi ya amsa tambayoyi kan cewa: “Shin shirin inganta sinadarin Uranium a Iran ya dawo? Shin har yanzu yana ci gaba, ko kuma barnar da aka yi wa Iran ya yi tsanani har ta kai ga dakatar da shi gaba daya?” Araqchi ya amsa da cewa; “Ba a daina bainganta sinadarin ba, duk da cewa barnar ta yi tsanani, amma duniya ta sani Iran ba za ta iya yin watsi da shirinta na inganta sinadarin Uranium ba saboda muhimmancinsa, domin wannan nasara ce ta masana kimiyyar kasar, kuma a halin yanzu abin alfahari ne ga kasa, kuma inganta sinadarin Uranium yana da matukar muhimmanci ga Iran.”

Da yake amsa tambayar cewa: “Mene ne dalilin da ya sa Iran ba za ta shigo da sinadarin uranium da ake inganta shi daga waje ba kamar yadda wasu kasashe ke yi? Araqchi ya ce: “Saboda wannan nasara ce ta ilimi, nasara ce da kasar Iran ta samu, to me ya sa za mu shigo da shi daga waje, duk da za ta iya samar da kanta?”.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Iraki Ta Yi Watsi Da Bukatar Amurka Akan Dakarun Sa Kai Na” Hashdus-sha’abi”
  • Gwamna Namadi Ya Amince Da Nadin Sabbin Sakatarori Guda Takwas
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Jaddada Hakkinta Na Tace Sinadarin Uranium A Cikin Kasarta
  • Pezeshkian: Tunanin Kawo Karshen Shirin Nukiliyar Iran Ya Yi Kama Da Tabuwa
  • Sheikh Qasem: Nuna Halin Ko In-Kula Na Duniya Ne Ya Jawo Kisan Kiyashi A Gaza
  • Gwamna Namadi Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Hukumar Hisba Ta Jihar Jigawa
  • Gwamna Namadi Ya Jinjinawa Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Bisa Ayyukan Raya Kasa
  • Hukumar Kashe Gobara Ta Jihar Kwara Ta Taimaka Wajen Hana Lalacewar Wani Bene A Ilorin
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce; Iran Ba Zata Bar Tace Sinadarin Uranium Ba
  • Jami’in Shari’ar Kasa Da Kasa Ya Bayyana Cewa: Harin Da Aka kai Kan Iran Babban Laifi Ne