Ana samun Karancin Masu Sayen Dabbobi A Kano Duk Karatowar Sallar Layya
Published: 3rd, June 2025 GMT
Dillalan rago a jihar Kano sun nuna damuwarsu kan rashin zuwan masaya da suke fuskanta duk da ‘yan kwanaki da suka rage ayi bukukuwan Sallah.
Ziyarar da aka kai kasuwar dabbobi ta Gandun Albasa ta nuna cewa, da yawa daga cikin masu sayar da kayayyaki sun shafe tsawon yini ba tare da yin cinikin komai ba, inda masu saye kadan ke zuwa sayen dabbobin hadaya.
Da yake zantawa da gidan rediyon Najeriya shugaban kasuwar dabbobi ta Gandun Albasa, Alhaji Yusuf Ahmed Muhammad ya bayyana cewa duk da cewa mutane na zuwa kasuwar domin tambayar farashin, amma a zahiri kadan ne ke saye.
Ya bayyana cewa yayin da wasu kwastomomi ke siyan kananan raguna da farashinsu ya kai tsakanin ₦80,000 zuwa 150,000, da yawa ba sa iya sayen manyan raguna.
A cewar Alhaji Yusuf, farashin raguna ya tashi daga ₦80,000 zuwa miliyan 1, shanu daga ₦250,000 zuwa miliyan 2, rakuma daga ₦500,000 zuwa ₦1 miliyan.
Ya kuma bukaci jama’a da su yi watsi da jita-jitar da ake ta yadawa game da tsadar kayayyaki, inda ya kara musu kwarin gwuiwa maimakon su ziyarci kasuwa su gani da kansu.
“Kamar yadda kuke gani mutane kadan ne ke tsaye kusa da wasu dabbobi suna neman farashi amma a karshe yawancinsu suna barin ba tare da siya ba”
Wani dillalin dabbobi, Alhaji Anas Garba Abubakar, ya bayyana cewa a shekarun baya miliyan 2 na iya sayen raguna sama da ashirin daga kasuwannin cikin gida. “Amma a wannan shekara, za ku iya samun kusan raguna biyar kawai a kan adadin,” in ji shi.
Ya alakanta tashin farashin da dalilai kamar hana shigo da rago daga Nijar da kuma tsadar kayan abinci da ake ci gaba da yi, wanda har yanzu ba a samu canji ba duk da faduwar farashin kayan abinci a fadin kasar.
Masu son siyan kayayyaki Abdullahi Kabir da Bashir Ibrahim Hassan su ma sun bayyana nasu bayan sun ziyarci kasuwar. “Mun zo nan don siyan raguna, amma kamar yadda kuke gani, dole ne mu koma gida mu sake shiryawa. Farashin ya yi tsada sosai.”
Sun bukaci gwamnati da masu ruwa da tsaki da su dauki matakin gaggawa don hana faruwar lamarin.
A al’adance dai, kwanaki masu gabatowa da Sallar Idi, kasuwannin dabbobi sun cika da masu saye da sha’awar sayen dabbobin hadaya.
KHADIJAH ALIYU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaba Tinubu Ya Karrama Bill Gates Da Lambar Girmamawa Ta CFR
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya karrama daya daga cikin masu kamfanin Microsoft, Bill Gates, da lambar girmamawa ta kasa — Commander of the Order of the Federal Republic (CFR), inda ya jaddada cewa Gates ya kasance abin koyi ga shugabanni a fadin duniya saboda yadda yake taimaka wa talakawa da masu bukata ta musamman.
Shugaban ya kuma bayyana cewa Mista Gates, wanda shi ne Shugaban Gidauniyar Melinda da Gates, ya bada gudummawa a fannonin kiwon lafiyar mata, noma da bincike kan cututtuka masu yaduwa.
Ya gode wa Bill Gates bisa gudummawar da yake bayarwa a duniya, musamman wajen saukaka rayuwa da kare lafiyar masu rauni da wadanda ke cikin bukata.
Ministan Lafiya da Ci gaban Jama’a, Farfesa Ali Pate, ya ce karramawar da aka yi wa Mista Gates ta cancanta kwarai, idan aka yi la’akari da irin gagarumar rawar da ya taka a ci gaban Najeriya.
Farfesa Pate ya bayyana cewa taimakon da Gidauniyar Bill da Melinda Gates ta bayar ya taimaka sosai wajen kawar da cutar shan inna (polio) a kasar.
Yayin da yake gode wa Shugaban Kasa bisa karramawar CFR, Mista Gates ya ce yaki da cutar shan inna daya ce daga cikin mafi wahala da Gidauniyarsu ta yi, sai dai hakan ya sa su hada kai da sarakunan gargajiya don cimma nasara.
Ya bayyana cewa Gidauniyar ta kaddamar da allurar rigakafin cutar HPB don rage mace-macen mata kimanin 7,000 a shekara sakamakon cutar sankarar mahaifa.
Mista Gates ya bayyana cewa allura guda daya kacal da ake bai wa ‘yan mata masu shekaru 9 zuwa 14 na iya basu kariya na daga cutar.
Gates ya tabbatar wa Shugaban Kasa cewa zai ci gaba da jajircewa wajen inganta lafiya a Najeriya, inda ya ce yana da niyyar amfani da dukiyarsa gaba daya wajen wannan aiki cikin shekaru ashirin masu zuwa.
Aliko Dangote, Shugaban Kamfanin Dangote, Ministan Harkokin Musamman da Hulda tsakanin Gwamnati, Zephaniah Jisalo, manyan jami’an Gidauniyar Gates, da Dakta Ayuba Burki Gufwan, Sakataren Gwamnati na Hukumar Kula da Masu Bukata ta Musamman na Kasa, na daga cikin wadanda suka halarci bikin karramawar.
Daga Bello Wakili