HausaTv:
2025-06-04@12:29:36 GMT

Arakci: Cinikayya A Tsakanin Iran Da Masar Za Ta Kara Bunkasa

Published: 2nd, June 2025 GMT

 Ministan harkokin wajen Jamhuriyar musuluinci ta Iran wanda ya kai Ziyarar aiki kasar Masar ya bayyana cewa, cinikayya a tsakanin kasashen biyu za ta karu.

Ministan harkokin wajen na Iran wanda ya gabatar da taron manema labaru na hadin gwiwa da takwaransa na kasar Masar ya ce: “A bisa yarjejeniyar da bangarorin biyu su ka cimmawa za a kara girman kasuwancin da ake tsakanin Iran da Masar.

Abbas Aragchi ya godewa mai masaukinsa na Masar Badar Abdulatif, saboda tattaunawa mai muhimmanci da su ka yi.”

Bugu da kari Abbas Arakci ya yi wa shugaban kasar Masar godiya saboda ganawa da ya yi da shi, yace: Wannan Shi ne ganawata ta hudu da shugaban da shi daga sheakarar da ta gabata’.

Har ila yau, ministan harkokin wajen na Iran ya yaba ganawar da aka yi a tsakanin shugabannin kasashen Iran da na Masar, a taron kungiyar kasashen musulmi da aka gudanar a bara. Sannan ya kammala da cewa wannan yana nuna irin muhimmancin da kasashen biyu suke daukar juna.

Da yake Magana akan yakin Gaza kuma, ministan harkokin wajen na Iran ya jinjinawa Masar da Qatar saboda kokarin da suke yi na ganin an dakatar da yaki.”

Dangane da tattaunawar Nukiliya tsakanin Iran da Amurka kuma, ministan harkokin wajen na Iran ya ce: Manufar tattaunawar ita ce tabbatar da cewa Iran baa ta nufin kera makamin Nukiliya, kuma akwai yiyuwar a kai ga cimma yarjejeniya.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Rikici Yana Ci Gaba Da Gudanar A Kasar Sudan Tsakanin Sojoji Da Dakarun Kai Daukin Gaggawa

Rikici tsakanin sojojin Sudan da dakarun kai daukin gaggawa na kasar yana ci gaba da habaka a wurare da dama na kasar

Kasar Sudan dai na fuskantar tabarbarewar harkokin tsaro cikin hanzari, a daidai lokacin da ake ci gaba da gwabza fada tsakanin sojoji da dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces (RSF), a cikin sarkakkiyar yanayin jin kai da na siyasa da kuma fadadan rikici a jihohi daban-daban.

Fadace-fadace a Sudan suna ci gaba da karuwa, inda ake ci gaba da gwabza fada tsakanin sojoji da mayakan kungiyar Rapid Support Forces, inda sojojin saman Sudan suka zafafa kai hare-hare ta sama ta hanyar amfani da jiragen sama marasa matuka ciki, kuma suka yi luguden wuta kan wasu muhimman wurare na kungiyar Rapid Support Forces a jihar Kordofan ta Arewa.

Hare-haren sun fi tsanani ne a yankin Kilo Zero dake arewacin Bara da Ummu Sayala, tare da lalata motocin soji da kayayyakin aiki, baya ga hasarar dimbin dakarun kungiyar Rapid Support Forces, kamar yadda majiyoyi da dama suka tabbatar da nasarar sojojin Sudan kan ‘yan tawaye.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Alakar Iran Da Lebanon Tarihi Ce Mai Tushe Da Ta Ginu Kan Mutunta Juna
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Soki Rahoton Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Ta Duniya Kan Kasarsa
  • Iran Ta Yi Watsi Da Da’awar Kungiyar Hadin Kan Kasashen Larabawa Na Da’awar Mallakar Wasu Yankunan Iran
  • Rikici Yana Ci Gaba Da Gudanar A Kasar Sudan Tsakanin Sojoji Da Dakarun Kai Daukin Gaggawa
  • Turkiya: An Bude Tattaunawa A Tsakanin Rasha Da Ukiraniya
  • Fira Ministan Kasar Senegal Yana Ziyarar Aiki A Kasashen Yammacin Afirka
  • Kasar Iran Ta Soki Rahoton Hukumar IAEA Na Baya-Bayan Nan Shirinta Na Makamashin Nukiliya
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Yana Ziyarar Aiki A Kasar Masar, inda Ya Gana Da Shugaban Kasar
  • Araghchi zai fara ziyarar kwanaki biyu a kasashen Masar da Lebanon