HausaTv:
2025-07-23@22:48:58 GMT

Arakci: Cinikayya A Tsakanin Iran Da Masar Za Ta Kara Bunkasa

Published: 2nd, June 2025 GMT

 Ministan harkokin wajen Jamhuriyar musuluinci ta Iran wanda ya kai Ziyarar aiki kasar Masar ya bayyana cewa, cinikayya a tsakanin kasashen biyu za ta karu.

Ministan harkokin wajen na Iran wanda ya gabatar da taron manema labaru na hadin gwiwa da takwaransa na kasar Masar ya ce: “A bisa yarjejeniyar da bangarorin biyu su ka cimmawa za a kara girman kasuwancin da ake tsakanin Iran da Masar.

Abbas Aragchi ya godewa mai masaukinsa na Masar Badar Abdulatif, saboda tattaunawa mai muhimmanci da su ka yi.”

Bugu da kari Abbas Arakci ya yi wa shugaban kasar Masar godiya saboda ganawa da ya yi da shi, yace: Wannan Shi ne ganawata ta hudu da shugaban da shi daga sheakarar da ta gabata’.

Har ila yau, ministan harkokin wajen na Iran ya yaba ganawar da aka yi a tsakanin shugabannin kasashen Iran da na Masar, a taron kungiyar kasashen musulmi da aka gudanar a bara. Sannan ya kammala da cewa wannan yana nuna irin muhimmancin da kasashen biyu suke daukar juna.

Da yake Magana akan yakin Gaza kuma, ministan harkokin wajen na Iran ya jinjinawa Masar da Qatar saboda kokarin da suke yi na ganin an dakatar da yaki.”

Dangane da tattaunawar Nukiliya tsakanin Iran da Amurka kuma, ministan harkokin wajen na Iran ya ce: Manufar tattaunawar ita ce tabbatar da cewa Iran baa ta nufin kera makamin Nukiliya, kuma akwai yiyuwar a kai ga cimma yarjejeniya.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Da Masar Za Su Karfafa Dangantakarsu Karkashin Kungiyar SCO

Su kuwa mahalarta taron, sun yaba da kyautatuwar dangantakar kasashen biyu da rawar da SCO ke takawa. Sun kuma bayyana fatan Masar da Sin za su yi amfani da damarmakin ci gaba da SCO ta samar domin su hada hannu tare, su inganta tsarin jagorantar harkokin duniya da farfadowar kasashe masu tasowa. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Yi Mu’amala Da Kasashen Dake Kan Karshen Kogin Yarlung Zangbo Dangane Da Batun Gina Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Karfin Ruwa A Kogin
  •  Iraki Ta Yi Watsi Da Bukatar Amurka Akan Dakarun Sa Kai Na” Hashdus-sha’abi”
  • Shugaban Amurka Trump Ya Bukaci Gurfanar Da Tsohon Shugaban Amurka Barack Obama A gaban Kuliya
  • Jami’an Kasashen Rasha, China, Iran Sun Gudanar Da Taron Hadin Gwiwa A Tehran
  • Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar
  • Fizishkiyan: Batun Kare Hakkin Bil’adama Ba Komai Ba Ne Sai Karya
  • Sin Da Masar Za Su Karfafa Dangantakarsu Karkashin Kungiyar SCO
  • Kasar Sin Na Fatan EU Za Ta Yi Aiki Da Ita Bisa Alkibla Guda Da Tsara Hadin Gwiwa Na Shekaru 50 Masu Zuwa
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce; Iran Ba Zata Bar Tace Sinadarin Uranium Ba
  • Ministocin Tsaron kasashen Rasha Da JMI Sun Hadu A Birnin Mosco