Turkiya: An Bude Tattaunawa A Tsakanin Rasha Da Ukiraniya
Published: 2nd, June 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Turkiya Hakan Fidan ya jaddada goyon bayan da kasarsa take bai wa tattaunawar da ake yi a tsakanin Rasha da Ukiraniya, ya kuma kara da cewa; Ana yin nazarin yadda za a gana, a kuma tattauna tsakanin shugabannin kasashen biyu.”
Fidan ya kuma bayyana fatansa na ganin cewa tattaunawar da aka bude a yau ta kai ga haifar da daa mai ido.
Haka nan kuma ya ce, kasarsa za ta yi duk abinda za ta iya, domin ganin cewa kasashen biyu sun kai ga cimma yarjejeniyar zaman lafiya a tsakaninsu.
Kafar watsa labaru ta Axios; ta ambato majiyar Ukiraniya na cewa, Rasha ta gabatar da tsarin zaman lafiya wanda ya kunshi yadda za a kawo karshen yaki.
A yau Litinin ne aka yi ganawa a tsakanin tawagogin kasashen biyu a birnin Istanbul domin lalubo hanyoyin zaman lafiya tsakanin Rasha da Ukraniya.
Gabanin zaman Istanbul dai, ministan harkokin wajen Rasha Sergey Lavrov ya ce; kasarsa tana da tsarin yadda za a kawo karshen yaki ta hanyar magance matsalar daga tushe.
Tattaunawar tana zuwa ne, kwana guda bayan da Ukiraniya ta kai wasu munanan hare-hare a yankuna masu nisa na cikin kasar Rasha da su ka hada da cibiyar muhimman jiragen Rasah masu kai hari a yankin Siberia tare da tashin gobara a cikin wasu jiragen.
Yankuna biyar ne dai a Rasha ,kasar Ukiraniya ta kai wa hare-hare daga ciki har da wurin da ya kai nisan kilo mita 4000 daga kan iyakar kasashen biyu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
Gwamnatin mamayar Isra’ila ta yanke hukuncin kisa kan masu fama da cutar kansa da kuma waɗanda suke fama da matsalar koda na mutuwa a Gaza domin hana fitar da su wata kasa don neman magani
Cibiyar Kare Hakkin Dan Adam ta Gaza ta bayyana matukar damuwarta game da tabarbarewar lafiyar marasa lafiya da ke fama da cutar kansa da kuma cutar koda a Zirin Gaza. Wadannan cututtuka sun kara ta’azzara ne sakamakon hare-haren sojojin mamayar Isra’ila kan Gaza da kuma ci gaba da killace yankin bayan tsagaita bude wuta, gami da hana shigar dq magunguna da kayayyakin ayyukan likitanci masu muhimmanci cikin yankin. Cibiyar ta kuma yi nuni da tsauraran matakan fitar da marasa lafiya zuwa ƙasashen waje don neman magani.
A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Lahadi, Cibiyar ta tabbatar da cewa, wannan yanayin ba shi da wata shakka cewa Isra’ila na aiwatar da manufar kisan gilla a kan dubban marasa lafiya ta hanyar hana su ‘yancinsu na rayuwa da magani da gangan, da kuma canza wahalarsu zuwa wani nau’in hukunci na gama gari.
Cibiyar ta ambaci majiyoyin lafiya da ke tabbatar da cewa, akwai marasa lafiya 12,500 da ke fama da cutar kansa a Zirin Gaza, ciki har da ƙananan yara. Ta lura cewa mata sun kai kusan kashi 52% na dukkan masu cutar kansa a Gaza.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasar Qatar Ta Ba Da Tallafin Gaggawa Ga Al’ummar Sudan Bayan Gumurzun El-Fasher November 2, 2025 IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya November 2, 2025 Amurka : zamu dauki matakin soja idan Najeriya ta gaza kawo karshen kashe Kiristoci November 2, 2025 Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza November 2, 2025 Wasu Yan Ta’adda Sun Kashe Dakarun Sa Kai 2 A Kudu Maso Gabashin Iran November 2, 2025 Sojojin Amurka Na Kara Fuskantar Venezuwela Adaidai Lokacin da Trump Ke Musanta Batun Kai Hari November 2, 2025 Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon November 2, 2025 Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya November 2, 2025 Shugaban AmurkaTrump ya yi barazanar daukar matakin soji kan Najeriya November 2, 2025 Kamaru: Jagroan ‘Yan Hamayya Ya Yi Kira Da A Tsayar Da Harkoki A Fadin kasar November 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci