HausaTv:
2025-07-24@03:48:54 GMT

Turkiya: An Bude Tattaunawa A Tsakanin Rasha Da Ukiraniya

Published: 2nd, June 2025 GMT

Ministan harkokin wajen Turkiya Hakan Fidan ya jaddada goyon bayan da kasarsa take bai wa tattaunawar da ake yi a tsakanin Rasha da Ukiraniya, ya kuma kara da cewa; Ana yin nazarin yadda za a gana, a kuma tattauna tsakanin shugabannin kasashen biyu.”

Fidan ya kuma bayyana fatansa na ganin cewa tattaunawar da aka bude a yau ta kai ga haifar da daa mai ido.

Haka nan kuma ya ce, kasarsa za ta yi duk abinda za ta iya, domin ganin cewa kasashen biyu sun kai ga cimma yarjejeniyar zaman lafiya a tsakaninsu.

 Kafar watsa labaru ta Axios; ta ambato majiyar Ukiraniya na cewa, Rasha ta gabatar da tsarin zaman lafiya wanda ya kunshi yadda za a kawo karshen yaki.

A yau Litinin ne aka yi ganawa a tsakanin tawagogin kasashen biyu a birnin Istanbul domin lalubo hanyoyin zaman lafiya tsakanin Rasha da Ukraniya.

 Gabanin zaman Istanbul dai, ministan harkokin wajen Rasha Sergey Lavrov ya ce; kasarsa tana da tsarin yadda za a kawo karshen yaki ta hanyar magance matsalar daga tushe.

Tattaunawar tana zuwa ne, kwana guda bayan da Ukiraniya ta kai wasu munanan hare-hare a yankuna masu nisa na cikin kasar Rasha da su ka hada da cibiyar muhimman jiragen Rasah masu kai hari a yankin Siberia tare da tashin gobara a cikin wasu jiragen.

Yankuna biyar ne dai a Rasha ,kasar Ukiraniya ta kai wa hare-hare daga ciki har da wurin da ya kai nisan kilo mita 4000 daga kan iyakar kasashen biyu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sheikh Qasem: Nuna Halin Ko In-Kula Na Duniya Ne Ya Jawo Kisan Kiyashi A Gaza

Sakatare-janar na kungiyar Hizbullah Sheikh Naim Qasem ya fitar da wata sanarwa inda ya yi kakkausar suka da Allah wadai da abin da ya bayyana a matsayin yakin kisan kare dangi da Amurka da Isra’ila ke yi wa al’ummar Palasdinu a Gaza, yana mai zargin kasashen duniya da yin shiru a kan laifukan da suka zarce dukkan matakan jin kai da kuma kyawawan dabi’u na ‘yan adataka.

“Abin da al’ummar Falasdinawan da ake zalunta ke jurewa a Gaza, tun daga cin zarafi na Amurka da Isra’ila, zuwa ta’addanci, kisan kiyashi, jefa su a cikin yunwa, da kashe jama’a, ya wuce duk wani mataki na lamirin dan adam,” in ji Sheikh Qassem.

Ya kuma yi kakkausar suka ga gazawar manyan kasashen duniya da gaza aiwatar da dokokin kasa da kasa, yana mai cewa, “Shiru da kasashen duniya suka yi, abin Allah wadai ne ga gwamnatocin kasashen duniya, musamman na kasashen musulmi da larabawa.

Da yake ishara da kiraye-kirayen baya-bayan nan da kasashe  sama da ashirin suka yi na a dakatar da yakin, Sheikh Qassem ya yi ishara da cewa irin wadannan kalamai da cewa ba su isa ba ko kadan, Ya ce, “bai isa ba a ce kasashe 25 sun yi kira da a dakatar da yakin Gaza, wannan furucin kadai bai wadatar ba.

Sheikh Qassem ya yi kira da a kakaba takunkumi kan “Isra’ila”,  da gurfanar da su a gaban shari’a, da kuma dakatar da duk wani nau’i na hadin gwiwa da ita.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Yi Mu’amala Da Kasashen Dake Kan Karshen Kogin Yarlung Zangbo Dangane Da Batun Gina Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Karfin Ruwa A Kogin
  •  Iraki Ta Yi Watsi Da Bukatar Amurka Akan Dakarun Sa Kai Na” Hashdus-sha’abi”
  • Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne
  • Sheikh Qasem: Nuna Halin Ko In-Kula Na Duniya Ne Ya Jawo Kisan Kiyashi A Gaza
  • Jami’an Kasashen Rasha, China, Iran Sun Gudanar Da Taron Hadin Gwiwa A Tehran
  • Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar
  • Hana Natasha Zaman Majalisa Barazana Ne Ga Dimokuraɗiyya — CLO
  • Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu
  • Gwamnatin Zamfara Ta Kira Babban Taron Tsaro Tare Da Bayyana Sabbin Dabaru Na Yakar ‘Yan Bindiga.
  • Ministocin Tsaron kasashen Rasha Da JMI Sun Hadu A Birnin Mosco