Mutuwar kasko: Mai gida da dan fashi sun kashe juna a Abuja
Published: 2nd, June 2025 GMT
Wani magidanci ya yi mutuwar kasko da wani mai sana’ar jari-bola, bayan da gungun wasu ’yan jari-bola suka yi kokarin cire tagar gidansa da karfin tsiya a yankin Babban Birnin Tarayya.
Magidancin, wanda ke sana’ar sayar da tufafin gwanjo ya gamu da ajalinsa ne bayan bata-garin sun caka masa wuka a yankin Tsohuwar Kutunku da ke Karamar Hukumar Gwagwalada.
Wani dan unguwar mai suna Francis Nnamdi, ya ce da misalin karfe 9.26 na dare ne wasu mutum uku masu sana’ar bola-jari suka je gidan mutumin, suna kokarin cire karfen tagarsa.
Ya ce cewa bayan mai gidan ya gan su ne ya tunkare su domin jin dalilinsu na neman cire masa tagogi, inda a garin haka daya daga cikinsu ya zaro wuka.
Ganin haka ne mutumin ya shiga daki ya dauko adda, kuma a garin rikicin masu bola-jarin suka caka masa wuka, shi kuma ya mayar da martani ta hanyar saran dayansu da addar hannunsa, ragowar kuma suka tsere, suka bar dayan kwance a cikin jini.
Ma’aikatan Kotu Koli sun janye yajin aikin da suka shirya tafiya Uba ya harbe ɗansa har lahira saboda zaton biri neYa ce daga bisani makwabta suka kira ’yan sanda, suka dauke gawarwakin zuwa Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abuja da ke Gwagwalada, inda likitoci suka sanar cewa dukkansu sun mutu, aka ajiye gawarwakin a mutuware.
Mun nemi karin bayani daga kakakin ’yan sanda na Babban Birnin Tarayya, SP Adeh Josephine, amma ta shaida wa wakilinmu cewa ba ta samu rahoton lamarin ba, amma za ta bincika.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Bola Jari Gwagwalada karfe
এছাড়াও পড়ুন:
Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya
Ranar Laraba, ruwan sama da hazo za su afkawa jihohin Zamfara, Adamawa, Kaduna, Sokoto, Kebbi da Taraba. Daga baya kuma, za a samu ruwan sama a jihohin Katsina, Bauchi da Sakkwato. Arewa ta rsakiya za ta fuskanci ruwan sama a Abuja, Nasarawa, Neja da Binuwe da safe, yayin da yamma za ta shafi Nasarawa, Filato, Kwara da Kogi.
A Kudu, ana hasashen ruwan sama da safe a Ogun, Ondo, Oyo, Edo, Enugu, Ebonyi, Cross River, Rivers da Akwa Ibom, sannan daga bisani a rana, za a sami ruwan sama a fadin yankin.
NiMet ta gargjama’a su ɗauki matakan kariya, musamman inda hadari zai faru, domin iska mai ƙarfi na iya gabatar da haɗari. An shawarci mutane su guji tuƙi a lokacin ruwan sama mai ƙarfi, su cire na’urori daga soket, su guji tsayuwa kusa da manyan itatuwa, sannan masu jirgin sama su nemi rahoton yanayi daga NiMet kafin tafiya. Ana kuma shawarci jama’a su dinga bin sahihan bayanan yanayi daga shafin NiMet:
www.nimet.gov.ng.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp