Ma’aikatan Kotu Koli sun janye yajin aikin da suka shirya tafiya
Published: 2nd, June 2025 GMT
Ma’aikatan shari’a a Kotun Koli da sauran kotuna sun jinginr shirinsu na fara yajin aiki daga yau Litinin 2 ga watan Yuni domin matsa lamba kan aiwatar da sabbin albashi.
Ma’aikatan, a karkashin kungiyar Ma’aikatan Shari’a ta Najeriya (JUSUN), sun ce sun janye shiga yajin aikin ne bayan wani taro da suka yi da Alkalin Alkalan Najeriya, Kudirat Kekere-Ekun inda aka ba su tabbaci mai ƙarfi.
Haka zalika, ma’aikatan Hukumar Shari’a ta Kasa (NJC) da Kotun Koli ta Tarayya (FHC) sun kuma yanke shawarar ba za su ci gaba da yajin aikin ba.
A cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na reshen NJC na JUSUN, Joel Ebiloma, ya bayar, ya ce kungiyar ta ba hukumomi wa’adin makonni biyu don ba su damar kintsawa don biyan buƙatunsu.
Uba ya harbe ɗansa har lahira saboda zaton biri ne Jirgin soji ya kashe ’yan sa-kai 20 da ke fatattakar ’yan bindiga a ZamfaraSanarwar ta ƙara da cewa an dakatar da yajin aikin ne domin bai wa Ofishin Akanta Janar na Tarayya damar fitar da kasafin kudi ga ɓangaren shari’a bisa kasafin kudin 2025 wanda ya haɗa da biyan bashin ƙarin albashi, mafi ƙarancin albashi, da kuma ƙarin kashi 25%/35% na albashi.
Sai dai, Kotun Koli a cikin wata sanarwa da ta fitar a ƙarshen taronta ta ce ma’aikatan sun cimma matsaya na ba za su shiga yajin aikin ba bayan nazarin batutuwan da ƙoƙarin CJN na biyan buƙatunsu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ma aikatan Shari a Yajin aiki yajin aikin
এছাড়াও পড়ুন:
Guardian: Isra’ila Tana Kai Wa Makarantun Dake Dauke Da ‘Yan Gudun Hijira a gaza Hari, Tana Sane Da Hakan
Jaridar Guardian ta ta kasar Birtaniya ta bada labarin cewa, Hare-haren da sojojin HKI su ka kai kan wata makaranta, inda yan gudun hijira Falasdinawa suke samun mafaka da gangan suka yi shi, suna sane, kuma a halin yanzu suna Shirin kai wa wasu makarantun guda 4 hare-hare nan gaba.
Jaridar ta kara da cewa: Isra’ila ta ayyana wasu Karin makarantu wadanda Falasdinawa suke samun mafaka a cikinsu domin kai musu hare-hare a nan gaba. A lokacinda HKI ta kasa ganin mayakan Hamas a fili sojojinta sun koma kan kissan Falasdinawa fararen hula, wadanda suke samun mafaka a makarantu.
A cikin watanni da suka gabata sojojin mamayar sun kai hare-hare akan wasu gine-ginen 6 wadanda suka kasance makarantu ne, wadanda Falasdinawa maza da mata da yara suka maidasu wuraren fakewa daga hare-haren sojojin HKI, suka kai mutane 120 ga shahada.
A ranar Litinin da ta gabata ce, sojojin mamayar suka kai wani harin a kan makarantar “A’ishiyya” wacce ta zama sansanin ‘yan gudun hijira a garin Deir-Balah’ na tsakiyar Gaza. Suka kuma kai falasdinawa da dama ga shahada.
Amma suka bada sanarwan cewa, ‘yan ta’adda ne suke fakewa a cikin makarantar, ba tare da sun gabatar da wata shaida ta tabbatar da hakan ba.
A bisa wani rahoton na MDD ta fitar, ta ce kaso 95% na makarantun Gaza, sun lalace, a yayin da wasu kimani 400 su ka rushe gaba daya saboda hare-haren sojojin yahudawan. A ranar 26 ga watan Mayu da ya shude ne, sojojin HKI suka kai hare-harei a kan makarantar “Fahmi-Jarjawi” da take cike da ‘yan gudun hijira wanda shi ma ya yi sanadiyyar shahadar Faladinawa da dama.