‘Yan Sanda Sun Kama Wani Gungun Masu Satar Motoci A Kwara
Published: 2nd, June 2025 GMT
Rundunar ‘Yan Sanda ta Jihar Nasarawa ta cafke wasu gungun masu satar motoci tare da dawo da wata mota da aka sace.
A cikin wata sanarwa da Jami’in hulɗa da jama’a na ‘yan sanda, SP Ramhan Nansel ya fitar, ya bayyana cewa jami’an ‘yan sanda sun kama wasu mutane huɗu da ake zargi da hannu a cikin wannan aika-aika, a kan hanyar Doma zuwa Lafia, bisa sahihan bayanan sirri.
Sanarwar ta kara da cewa, ana zargin waɗanda ake tuhuma da haɗa kai wajen satar mota da bindiga a Jihar Enugu, inda suka kwace wata mota kirar Toyota Venza mai launin baki da karfin bindiga.
Sanarwar ta bayyana cewa, saboda saurin tattara bayanan sirri da haɗin gwiwar jihohi ba tare da tangarda ba, an kama waɗanda ake zargin a yankin hanyar Doma zuwa Lafia, kuma an gano motar da aka sace nan take.
Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar, CP Shattima Jauro Mohammed, ya bayyana wannan nasara a matsayin babban ci gaba a yaƙi da satar motoci da aka tsara, inda ya jaddada kudirin rundunar wajen ganin cewa an dakile miyagun laifuka cikin gaggawa kuma an gurfanar da masu laifi.
Ya yabawa ƙwazon jami’an da suka gudanar da wannan aiki tare da tabbatarwa al’umma cewa rundunar ‘yan sanda za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.
Waɗanda ake zargin suna tsare a halin yanzu, kuma ana ci gaba da gudanar da bincike don gano sauran abokan aikinsu da kuma gano sauran abubuwan da aka sace.
Daga Aliyu Muraki
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kwara Satar Mota
এছাড়াও পড়ুন:
Netanyahu: Ba Za Mu Daina Yakin Gaza Ba
Fira ministan HKI wanda kotun duniya ta manyan laifuka take nem ruwa a jallo ya bayyana cewa; Babu yadda za su tsayar da yakin Gaza, matukar kungiyar Hamas ba ta mika wuya baki day aba.
Benjemine Netanyahu ya kuma ce; A lokacin da Hamas za ta mika makamanta ne, shi ne za mu yi tunanin ko za mu bude mata hanyar ficewa daga Gaza, da kuma dakatar da yaki.
A gefe daya tashar talabijin din CNN ta ambato wata majiya ta gwamnatin Amurka tana cewa; Amurka ta gargadi kungiyar Hamas akan cewa, hakurinta ya kusa karewa akan batun tsagaita wuta, tare da neman kungiyar ta gwagwarmaya ta bayar da jawabi a cikin gaggawa kafin makwanni biyu masu zuwa.
Tashar talabijin din CNN din ta kuma bayyana cewa; Amurkan ta bai wa Hamas lamunin cewa Isra’ila ba za ta shiga cikin tattaunawar kawo karshen yaki ba a tsawon lokacin dakatar da yaki da zai dauki kwanaki 60.
Sai dai kuma majiyar ta fada wa tashar talabijin din CNN cewa, Amurkan za ya janye wannan lamunin idan har kungiyar ta Hamas ba bayar da jawabi a cikin sauri ba.
Sai dai kuma masu bin diddigin abubuwan da suke faruwa sun bayyana cewa; HKI ce ummul-haba’isin tsaikon da ake samu a tsagaita wutar yakin ba kungiyar gwgawarmaya ta Hamas ba.
A nata gefen kungiyar Hamas ta ce, a mataki na baidaya kungiyar tana son ganin an tsagaita wuta, duk da cewa jagorancin kungiyar na Gaza ne zai yanke hukunci na karshe.Khalilul Hayya wanda ya bayyana hakan ya kara da cewa; Jagororin Hamas na cikin gida ne ke da alhakin aiwatar da duk wani mataki na tsagaita wuta, don haka su ne za su bayyana mataki na karshe.