‘Yan Sanda Sun Kama Wani Gungun Masu Satar Motoci A Kwara
Published: 2nd, June 2025 GMT
Rundunar ‘Yan Sanda ta Jihar Nasarawa ta cafke wasu gungun masu satar motoci tare da dawo da wata mota da aka sace.
A cikin wata sanarwa da Jami’in hulɗa da jama’a na ‘yan sanda, SP Ramhan Nansel ya fitar, ya bayyana cewa jami’an ‘yan sanda sun kama wasu mutane huɗu da ake zargi da hannu a cikin wannan aika-aika, a kan hanyar Doma zuwa Lafia, bisa sahihan bayanan sirri.
Sanarwar ta kara da cewa, ana zargin waɗanda ake tuhuma da haɗa kai wajen satar mota da bindiga a Jihar Enugu, inda suka kwace wata mota kirar Toyota Venza mai launin baki da karfin bindiga.
Sanarwar ta bayyana cewa, saboda saurin tattara bayanan sirri da haɗin gwiwar jihohi ba tare da tangarda ba, an kama waɗanda ake zargin a yankin hanyar Doma zuwa Lafia, kuma an gano motar da aka sace nan take.
Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar, CP Shattima Jauro Mohammed, ya bayyana wannan nasara a matsayin babban ci gaba a yaƙi da satar motoci da aka tsara, inda ya jaddada kudirin rundunar wajen ganin cewa an dakile miyagun laifuka cikin gaggawa kuma an gurfanar da masu laifi.
Ya yabawa ƙwazon jami’an da suka gudanar da wannan aiki tare da tabbatarwa al’umma cewa rundunar ‘yan sanda za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.
Waɗanda ake zargin suna tsare a halin yanzu, kuma ana ci gaba da gudanar da bincike don gano sauran abokan aikinsu da kuma gano sauran abubuwan da aka sace.
Daga Aliyu Muraki
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kwara Satar Mota
এছাড়াও পড়ুন:
Tsohon Jami’in Gwamnatin Biden Na Amurka Ya Tabbatar Da Cewa Isra’ila Ta Tafka Laifukan Yaki
Daya daga cikin manyan-manyan jami’an gwamnatin tsohon shugaban kasar Amurka Joe Biden, ya bayyana cewa: “Babu tantama gwamnatin HK Isra’ila ta tafka laifukan yaki a kan Falasdinawa a zirin Gaza da ta killace.
Matthew Miller wanda ya yi aiki a matsayin kakakin ma’aikatar harkokin wajen Amurka tun daga 2023 har zuwa karshen gwamnatin Joe Biden, ya fada wa tashar talabijin ta Sky News kan cewa; Isra’ilan ta tafka laifukan yaki.
Da aka yi masa tambaya a kan yakin Gaza a fadar White House, Miller ya ce; An yi ta samun tsabani dangane da yakin, sabani manya-manya wani lokacin kuma kananan sabani, kan yadda za a kare dangantakar Amurka da HK Isra’ila duk tare da abinda take aikatawa.”. Amma Miller ya tabbatar da cewa HK Isra’ilan ta tafka laifukan yaki wanda babu shakka a cikin hakan..
Da aka tambaye shi a kan, ko me ya sa a lokacin suke Mulki bai bayyana cewa HK Isra’ila tana aikata laufkan yaki ba? Sai ya amsa da cewa:
“Idan mutum yana cikin gwamnati, ba ya bayyana ra’ayinsa na kashin kansa, yana bayyana ra’ayin gwamnatin Amurka ne.”
Haka nan kuma ya ce; Aikin mai magana da yawun gwamnati, ko dai ka zama mai Magana da yawun shugaban kasa, ko gwmanatin kasar, amma idan baka cikin gwamnati, to za ka iya fadar ra’ayinka.”