Nukiliya : Iran ta gargadi kasashen yamma akan daukar duk wani irin mataki kan ta
Published: 2nd, June 2025 GMT
Iran ta gargadi kasashen yamma aka daukar duk wani irin mataki kan ta a daidai lokain da ake shirin gudanar da taron gwamnonin hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya a mako mai zuwa.
Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran mai kula da harkokin shari’a da na kasa da kasa ya yi watsi da rahoton da hukumar ta IAEA ta fitar kan shirin nukiliyar Iran na zaman lafiya, yana mai gargadin daukar matakin da ya dace.
Kazem Gharibabadi ya yi wadannan kalamai ne, bayan da hukumar ta IAEA ta yi zargi a cikin wani rahotonta na sirri ga kasashe mambobinta cewa Iran ta gaza bayar da rahoton ayyukanta na nukiliya a wasu wurare uku da ba a bayyana ba, tare da bayyana damuwarta game da tarin uranium da ake zargin an wadatar da shi zuwa kashi 60 cikin dari.
Ya ce rahoton ya dogara ne kan “jerin bayanan karya da gwamnatin sahyoniya ta bayar” tun sama da shekaru ashirin.
Ya kara da cewa, an yi watsi da dukkan tuhume-tuhume kan ayyukan nukiliyar Iran da suka gabata a karkashin kudurin kwamitin sulhu na MDD mai lamba 2231, wanda a hukumance ya amince da yarjejeniyar nukiliyar Iran ta 2015.
Gharibabadi ya kuma lura cewa rahoton na hukumar ya sake nuna yadda IAEA ke siyasantar da ayyukanta a kan Iran.
Ya sake nanata cewa “Iran ba ta neman makaman nukiliya kuma ba ta da wani makaman nukiliya.” Kamar yadda ake ta yayatawa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Makami Mai Linzami Daga Yemen Ya Tashi Jiniyar Gargadi A Garuruwa 300 Na HKI
Sa’oi kadai da su ka gabata jiniyar gargadi ta kada a cikin garuruwa da sansanonin ‘yan share wuri zauna 300 a HKI saboda makami mai linzami da mutane Yemen su ka harba.
Kafafen watsa labarun ‘yan sahayoniya sun ambaci cewa; an rufe filin saukar jiragen saman a “Ben Gorion” da kuma dakatar da kai da komowar jiragen sama.
Kafafen watsa labarun na HKI sun ambaci cewa; Miliyoyin mutane ne su ka gudu zuwa Mabuya.
Wannan sabon harin dai na sojojin Yemen yana zuwa ne a karkashin abinda sojojin na Yemen su ka kira, kakaba takunkumi na sama da ruwa akan HKI, tare da yin kira ga kamfanonin jiragen sama da na ruwa da su kauracewa zuwa wannan haramtacciyar kasa.
Filin saukar jiragen sama na Ben Gorion’ da tashoshin jiragen ruwa ta Haifa da Eiliat su ne wadanda takunkumin na sojojin Yamen ya fi shafa.
Kwanaki kadan da su ka gabata jagoran kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen, Sayyid Abdulmalik al-Husi ya sanar da cewa, ba za su daina kai wa HKI hare-hare, har sai idan sun kawo karshen yakin Gaza da kuma killace yankin da aka yi.