Sojojin mamayar Isra’ila sun kai hari kan fararen hula da suka yi tawaga zuwa wajen raba kayan agajin jin kai a garin Rafah

Rahotonni sun bayyana cewa: A rana ta biyu a jere, sojojin mamayar Isra’ila suna ci gaba da aiwatar da kisan kiyashi kan al’ummar zirin Gaza da ke fama da yunwa.

Shafin yanar gizo na Falestine Today ya watsa rahoton cewa: A safiyar yau Litinin 2 ga watan Yunin shekara ta 2025, sojojin mamayar Isra’ila sun aiwatar da wani sabon laifi ta hanyar kai hare-hare kan Falasdinawa a kusa da cibiyar bada agajin Amurka da ke birnin Rafah.

Ya zuwa yanzu dai wannan aika-aika ya yi sanadin shahadan Falasdinawa 3 tare da raunata wasu 60, ba a ma maganar laifin da aka aikata jiya a gaban duniya, inda aka zubar da jinin al’umma sama da 30 da kuma jikkata wasu daruruwa na daban a wurin karbar agajin abinci.

Majiyoyin cikin gida sun tabbatar da cewa: An kai wa daruruwan Falasdinawa hare-hare ne a lokacin da suke kan hanyarsu ta zuwa cibiyar ba da agaji da ke Rafah, inda hare-haren suka yi sanadaiyyar shahadar Falasdinawa 3, sannan wasu fiye da 60 suka jikkata.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Isra ila sun

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Yi Watsi Da Da’awar Kungiyar Hadin Kan Kasashen Larabawa Na Da’awar Mallakar Wasu Yankunan Iran

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya jaddada cewa: Tsibiran guda uku na Tunb Babba da Tunb Karami da Abu Musa yankuna ne Iran

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya yi watsi da ikirari da kungiyar hadin kan kasashen Larabawan yankin tekun Fasha (PGCC) ta yi dangane da tsibiran Iran guda uku, yana mai jaddada cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta dauki dukkan matakan da suka dace don tabbatar da tsaro da muradun kasar a cikin tsibiran guda uku.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Iran ya jaddada matsayin Jamhuriyar Musulunci ta Iran tare da yin watsi da ikirarin da ke kunshe a cikin bayanin karshe na taron ministocin harkokin wajen kasashen yankin tekun Fasha karo na 64 dangane da tsibiran kasar Iran guda uku na Tunb Babba, Tunb Karami da Abu Musa.

Baqa’i ya yi watsi da zarge-zargen da ke kunshe cikin wannan bayani dangane da hukunci da matakan shari’a da hukumomin Iran da abin ya shafa suka dauka dangane da tsibiran da aka ambata, yana mai cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta dauki duk wani matakin da ya dace don tabbatar da tsaro da muradun kasar a cikin tsibiran guda uku, da suka hada da filayenta, ruwa, da sararin samaniyarta, daidai da hakkinta na ‘yancin kai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Guardian: Isra’ila Tana Kai Wa Makarantun Dake Dauke Da ‘Yan Gudun Hijira a gaza Hari, Tana Sane Da Hakan
  • Tsohon Jami’in Gwamnatin Biden Na Amurka Ya Tabbatar Da Cewa Isra’ila Ta Tafka Laifukan Yaki
  • Iran Ta Yi Watsi Da Da’awar Kungiyar Hadin Kan Kasashen Larabawa Na Da’awar Mallakar Wasu Yankunan Iran
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Aiwatar Da Wani Kisan Kiyashi Kan Masu Bukatar Kayan Agaji
  • Jiragen Yakin NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 20, ‘Yan Banga 2 A Zamfara
  • Shafin Watsa Labaran Amurka Ya Bankado Illar Da Sojojin Yemen Suka Yi Wa Jirgin Truman Na Amurka
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hare-Hare Kan Filin Jirgin Saman Ben Gurion A Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Saudiyya : Matakin Isra’ila na hana mu ziyaratar falasdinwa, watsi ne da tayin zaman lafiya
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Yankunan Kasar Siriya Tare Da Kafa Wuraren Bincike