HausaTv:
2025-06-03@10:08:08 GMT

Za A Fassara Hudubar Hawan Arfa Da Harsunan Hausa Da Filatanci

Published: 1st, June 2025 GMT

 Mahukuntan kasar Saudiyya sun sanar da cewa a ranar hawan arfa na bana, za a fassara hudubar da za a yi da harsuna 34 daga cikinsu da akwai Hausa da filatanci.

Wasu harsunan Afirka da za a fassara hudubar ta Arfa da su, sun hada yarabanci, Sawahili, Somali da kuma Amharic na kasar Habasha.

A bisa sanarwar da kasar Saudiyya ta yi na ganin watan zulhijja, a ranar 27 ga watan Mayu, za a yi hawan Arfa a ranar 5 ga watan na Mayu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Wata hajiyar Najeriya daga Filato ta rasu a Makkah

Wata hajiyar Najeriya daga Jihar Filato ta rasu a birnin Makkah na ƙasar Saudiyya.

Hajiya Jamila Muhammad ta rasu ne a yayin da alhazai ke shirin fara gudanar da aikin Hajji gadan-gadan.

Sakataren Hukumar Kin Dadin Alhazai ta Jirage Filato, Daiyabu Dauda, ya sanar a ranar Litinin cewa Hajiya Jamila ta rasu ne a asibitin Sarki Abdulaziz da ke Makkah, sakamakon tashin cutar suga.

Ya ce Amirul Hajj na jihar da wasu manyan jami’ai sun halarci jana’izar marigayiyar, kamar yadda Musulunci ta tanada.

Yadda magidanci ya kuɓuta bayan wata 7 a hannun ’yan bindiga NAJERIYA A YAU: Hanyoyin kauce wa ɓarnar ambaliyar ruwa Hajji ta bayan fage: Saudiyya ta hana mahajjata 269,000 shiga Makka

Da rayuwarta, yawan alhazan Najeriya da suka rasu a aikin Hajjin bana ya ƙaru zuwa mutum uku.

Kafin ita, Najeriya ta rsa alhazai biyu da suka hada da Hajiya Adizatu Dazumi daga Jihar Edo da kuma  Alhaji Saleh Saleh daga Jihar Abiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet
  • Wata hajiyar Najeriya daga Filato ta rasu a Makkah
  • Babbar Sallah: Gwamnatin Kano ta ba makarantu hutun kwana 10
  • Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara
  • NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar
  • Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22 Da Suka Rasu
  • MDD : Gaza na cikin bala’i mafi muni tun soma yaki a Zirin a Oktoban 2023
  • Za a gabatar da Huɗubar Ranar Arfa a harsunan Najeriya 3
  • Za a ɗauke ruwan famfo na tsawon mako 2 a Abuja