HausaTv:
2025-06-03@09:57:25 GMT

 Za A Yi Taron Kasa Da Kasa Akan Mahangar Imam Khumaini Dangane Da Falasdinu

Published: 1st, June 2025 GMT

 A gobe Litinin ne dai za a bude taron karawa juna sani anan Tehran mai taken; Imam Khumaini da batun Falasdinu” wanda zai sami halartar masana na cikin gida da kuma waje.

Jawabin bude taro zai fito ne daga shugaban kungiyar kare hakkokin al’ummar Falasdinu, Hujjatul-Islam Muhammad Hassan Rahimiyan, haka nan kuma magajin garin Tehran Ali Ridha Zakani zai gabatar da jawabi.

 Bugu da kari a yayin wannan taron za a girmama jagororin gwgawarmaya da su ka yi shahada da su ka hada, Sahid Sayyid Hassan Nasrallah, shahid Isma’ila Haniyya, sai shahid Yahya Sinwar. Shi ma shugaban kungiyar Ansarullah ta Yemen Sayyid Abdulmalik Husi yana cikin wadanda taron na Tehran za karrama.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Turkiya: An Bude Tattaunawa A Tsakanin Rasha Da Ukiraniya

Ministan harkokin wajen Turkiya Hakan Fidan ya jaddada goyon bayan da kasarsa take bai wa tattaunawar da ake yi a tsakanin Rasha da Ukiraniya, ya kuma kara da cewa; Ana yin nazarin yadda za a gana, a kuma tattauna tsakanin shugabannin kasashen biyu.”

Fidan ya kuma bayyana fatansa na ganin cewa tattaunawar da aka bude a yau ta kai ga haifar da daa mai ido.

Haka nan kuma ya ce, kasarsa za ta yi duk abinda za ta iya, domin ganin cewa kasashen biyu sun kai ga cimma yarjejeniyar zaman lafiya a tsakaninsu.

 Kafar watsa labaru ta Axios; ta ambato majiyar Ukiraniya na cewa, Rasha ta gabatar da tsarin zaman lafiya wanda ya kunshi yadda za a kawo karshen yaki.

A yau Litinin ne aka yi ganawa a tsakanin tawagogin kasashen biyu a birnin Istanbul domin lalubo hanyoyin zaman lafiya tsakanin Rasha da Ukraniya.

 Gabanin zaman Istanbul dai, ministan harkokin wajen Rasha Sergey Lavrov ya ce; kasarsa tana da tsarin yadda za a kawo karshen yaki ta hanyar magance matsalar daga tushe.

Tattaunawar tana zuwa ne, kwana guda bayan da Ukiraniya ta kai wasu munanan hare-hare a yankuna masu nisa na cikin kasar Rasha da su ka hada da cibiyar muhimman jiragen Rasah masu kai hari a yankin Siberia tare da tashin gobara a cikin wasu jiragen.

Yankuna biyar ne dai a Rasha ,kasar Ukiraniya ta kai wa hare-hare daga ciki har da wurin da ya kai nisan kilo mita 4000 daga kan iyakar kasashen biyu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Bayar Da Shawarar Kafa Bankin Hadin Gwiwa Na Kasashen Kungiyar Shangai
  • Turkiya: An Bude Tattaunawa A Tsakanin Rasha Da Ukiraniya
  • Shettima: Shekaru Biyu Na Mataimaki, Jagora Mai Hangen Nesa Da Kawo Sauyi Nagari
  • Najeriya: An Bude Bincike Sojojin Da Suke Bayar Da Makamai Ga Kungiyoyi Masu Dauke Da Makamai
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ta Iran Ya Ce: Taron Kungiyar BRICS Zai Kawo Bunkasar Tattalin Arziki
  • ECOWAS Da CORET Sun Shirya Taro Domin Cigaban Makarantun Fulani A Kaduna
  • Nukiliya : Tehran ta soki rahoton IAEA da cewa bai da tushe
  • Gwamnonin Najeriya Sun Bayyana Alhininsu Bisa Rasuwar ‘Yan Wasan Kano
  • ‘Yan Gwagwamayar Falasdinu Sun Halaka Sojojin Mamayar Isra’ila Masu Yawa A Wani Harin Kwanton Bauna