Aminiya:
2025-05-01@00:54:46 GMT

’Yan adawa sun shirya ƙalubalantar Tinubu a zaɓen 2027 – Atiku

Published: 20th, March 2025 GMT

Tsohon mataimakin shugaban Nijeriya, Atiku Abubakar ya bayyana cewa yanzu haka ’yan adawar siyasa a ƙasar nan a shirye suke su ƙalubalanci shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaɓen shugaban ƙasa na 2027.

Tun bayan da ya sha kaye a zaɓen shugaban ƙasa na 2023, Atiku ya riƙa yin taro da ’yan adawa don neman karɓe mulki daga hannun jam’iyya mai ci.

Gobara ta ƙone gidaje tare da asarar dukiya a Gombe Gwamnan riƙon ƙwarya na Jihar Ribas ya isa gidan gwamnati

Da yake jawabi ga manema labarai tare da wasu ’yan adawa a zauren taro na ‘Yar’adua Center da ke Abuja a ranar Alhamis, Atiku ya ce an yi taron ne don sake samar da wasu ‘yan adawa kafin babban zaɓe mai zuwa.

Da yake amsa tambayoyi kan ko taron manema labarai na ƙawancen ‘yan adawa na nuni da haɗuwar jiga-jigan ‘yan adawa? Atiku ya ce, “Wannan ita ce samar da haɗakar ‘yan adawa gabanin 2027”.

A ranar Talata ne shugaba Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci a Jihar Ribas, inda ya kori gwamnan jihar Siminalayi Fubara da mataimakiyarsa da ’yan majalisar dokokin jihar, lamarin da ya sa ’yan adawa suka mayar da martani.

Da yake jawabi ga manema labarai a madadin shugabannin adawa a a zauren taron a Abuja, ranar Alhamis Atiku ya zargi Tinubu da son zuciya.

Sauran jiga-jigan ’yan adawa da suka halarci taron manema labarai sun haɗa da: Tsohon Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP a 2023, Peter Obi, wanda Yunusa Tanko ya wakilta, tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir Lawal, tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, sakataren haɗakar jam’iyyun siyasa na ƙasa, Peter Ameh, da dai sauransu.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Atiku Abubakar Babachir Lawal manema labarai

এছাড়াও পড়ুন:

Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce za a yi taro karo na hudu na shawarwari tsakanin Tehran da Washington kan shirin nukiliyar Jamhuriyar Musulunci ta Iran a birnin Rome na kasar Italiya a ranar Asabar mai zuwa.

M. Araghchi ya fadawa manema labarai a gefen taron majalisar ministocin gwamnatin kasar na mako-mako yau Laraba cewa, inda ya ce taron na Rome zai kasance gabanin wani taro a ranar Juma’a na tsakanin Tehran da kasashen Turan nan uku da ake wa lakabi da E3 wato – Ingila, Faransa da kuma Jamus wadanda suka sanya hannu kan yarjejeniyar nukiliyar Iran ta 2015.

Ya ce rawar da kasashen Turai uku ke takawa ta ragu sakamakon manufofinsu a tattaunawar da aka dade ana yi, don haka a shirye muke mu gudanar da zagaye na gaba na shawarwari da su a birnin Rome.

Babban jami’in diflomasiyyar ya kara da cewa, Tehran na da burin warware batun nukiliyarta cikin lumana.”

Da aka tambaye shi game da halin da ake ciki na baya-bayan nan na kudaden da Iran ta toshe saboda takunkumin da kasashen yamma suka kakaba mata, Araghchi ya ce daskararrun kudaden na daga cikin takunkumin da ya zama dole a dagewa iran.

Kawo yanzu Iran da Amurka sun yi tattaunawa har uku ta farko a Oman, ta biyu a Italiya sai kuma wace aka gudanar a ranar Asabar data gabata a Oman.

Dukkanin bangarorin na cewa akwai fata mai kyau a jerin tattaunawar da suka gabata.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Najeriya Wajen Yin Watsi Da Kariyar Cinikayya Da Yin Adawa Da Danniya Da Cin Zarafi
  • Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
  • Gwamnan Sokoto Ya Amince Da Sauya Wa Manyan Sakatarori 25 Ma’aikatu A Jihar 
  • Tinubu zai ziyarci Katsina
  • Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya
  • Rawar da Arewa za ta taka a Zaɓen 2027
  • Shugaba Tinubu Ya Taya Sabon Firaiministan Kanada Mark Carney Murna
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Shirya Fara Tantance ‘Yan Fansho
  • Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
  • Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara