’Yan adawa sun shirya ƙalubalantar Tinubu a zaɓen 2027 – Atiku
Published: 20th, March 2025 GMT
Tsohon mataimakin shugaban Nijeriya, Atiku Abubakar ya bayyana cewa yanzu haka ’yan adawar siyasa a ƙasar nan a shirye suke su ƙalubalanci shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaɓen shugaban ƙasa na 2027.
Tun bayan da ya sha kaye a zaɓen shugaban ƙasa na 2023, Atiku ya riƙa yin taro da ’yan adawa don neman karɓe mulki daga hannun jam’iyya mai ci.
Da yake jawabi ga manema labarai tare da wasu ’yan adawa a zauren taro na ‘Yar’adua Center da ke Abuja a ranar Alhamis, Atiku ya ce an yi taron ne don sake samar da wasu ‘yan adawa kafin babban zaɓe mai zuwa.
Da yake amsa tambayoyi kan ko taron manema labarai na ƙawancen ‘yan adawa na nuni da haɗuwar jiga-jigan ‘yan adawa? Atiku ya ce, “Wannan ita ce samar da haɗakar ‘yan adawa gabanin 2027”.
A ranar Talata ne shugaba Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci a Jihar Ribas, inda ya kori gwamnan jihar Siminalayi Fubara da mataimakiyarsa da ’yan majalisar dokokin jihar, lamarin da ya sa ’yan adawa suka mayar da martani.
Da yake jawabi ga manema labarai a madadin shugabannin adawa a a zauren taron a Abuja, ranar Alhamis Atiku ya zargi Tinubu da son zuciya.
Sauran jiga-jigan ’yan adawa da suka halarci taron manema labarai sun haɗa da: Tsohon Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP a 2023, Peter Obi, wanda Yunusa Tanko ya wakilta, tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir Lawal, tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, sakataren haɗakar jam’iyyun siyasa na ƙasa, Peter Ameh, da dai sauransu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Atiku Abubakar Babachir Lawal manema labarai
এছাড়াও পড়ুন:
Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole
“Ta yaya Jonathan zai zama barazana? Mun doke shi a baya lokacin da PDP take kan mulki.
“Idan mutum yana ganin cewa PDP ita ce kololuwar jam’iyya a Nijeriya, kuma ya sha kaye a lokacin da yake ganiyarsa, ina ganin sai makiyinsa ne kawai zai tilasta masa ya kara tsayawa takara a zaben 2027,” in ji shi.
Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa ya ce a yanzu haka Jonathan ya kasance dan siyasa mai daraja, yana mai cewa komawa fagen siyasa na iya rage masa kima da kuma zubar masa da darajar da yake da shi a idon duniya.
Ya jaddada cewa Jonathan ya samu damar nuna cewa mulki bai tsole masa ido ba, domin haka ne ya samu daraja a cikin harkokin siyasar Nijeriya, sake dawowa takara zai zubar masa da daraja.
Oshiomhole ya jaddada cewa, “Da zan iya ba shi shawara, zan cewa, ka ci gaba da rike matsayin. Ka yi mulki har na tsawon shekaru takwas, ba lallai ba ne ka sake yin mulki na shekara tara.”
ShareTweetSendShare MASU ALAKA