Jakadan Amurka a Najeriya, Richard Mills Jr, ya ziyarci mai martaba Sarkin Zazzau Malam Ahmad Bamalli domin ingantawa da karfafa hadin kan al’adu.

 

Jekadan ya ce Amurka ta jajirce sosai kan alakar da Najeriya ya kara da cewa; ‘ muna so mu zurfafa shi kuma mu ƙarfafa shi.”

 

A cewarsa, hanyar da ta fi dacewa wajen zurfafa wannan alaka ita ce ta haduwa irin wannan da za mu ji ta bakin juna.

 

“Ina sa ran jin ta bakinku kan abubuwan da kuke yi na karfafa hadin kan addini a tsakanin al’umma, damar ilimi da kuma damar yin aiki ga jama’ar ku.

 

“Abin da Amurka za ta iya yi don haɓaka ƙarin alaƙa da kuma matakan da za mu iya ɗauka don zurfafa dangantakarmu,” in ji Mills.

 

Da yake mayar da jawabi, Mai martaba Sarkin Zazzau ya yabawa ma’aikatar harkokin wajen Amurka kan bude cibiyar kula da harkokin a Amurka a jami’ar Ahmadu Bello.

 

Bamalli ya yi fatan wannan cibiar da aka kira da Window on America da turanci ta zama matakin samar da ingantacciyar dama tsakanin Amurka da masarautar Zazzau da jihar Kaduna.

 

Ya kara da cewa masarautar na da alaka mai tsawo da ofishin jakadancin Amurka inda ya kara da cewa tawagogin ofishin jakadanci sun kasance suna halartar Dabar karshen watan Ramadan a Zariya.

 

“Amma hakan ya tsaya cik tsawon wasu shekaru saboda rashin tsaro, amma za mu iya cewa zaman lafiya ya dawo ga al’ummarmu.

 

“Saboda haka, muna fatan mambobin ofishin jakadancin da sauran jami’an diflomasiyya za su ci gaba da halartar bukukuwan Sallah Durbar,” in ji Bamalli.

 

COV/ Ibrahim Suleiman

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya gana da Janar Christopher Musa bayan Ministan Tsaro ya yi murabus

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi wata ganawar sirri da tsohon Babban Hafsan Tsaron Najeriya, Janar Christopher Gwabin Musa a Fadar Shugaban Kasa.

Ganawar Tinubu da Janar CG Musa ya auku ne a ranar Litinin da dare, jim kadan kafin sanarwar murabus din Ministan Tsaro, Alhaji Muhammad Badaru Abubakar.

Majiyoyi na cewa gananawar shugaban kasa da Janar CG Musa na da nasaba da shirin shugaban kasar na cike gurbin da Badaru ya bari da kuma garambawul a shugabancin tsaron Najeriya.

Mai magana da yawun shugaban kasa Bayo Onanuga ya sanar cewa Badaru ya yi murabus ne saboda dalilai na rashin lafiya.

An kama ’yan bindiga 4 a Kano MAAUN: Ƙungiyar iyaye ta musanta zargin ƙara ƙudin yaye ɗalibai a jami’ar

Badaru ya ajiye aiki ne a daidai lokacin da Najeriya ke fama da karuwar matsalar tsaro musammana a shiyyar Arewa lamarin da ya sa Shugaba Tinubu ya ayyan dokar ta-baci kan sha’anin tsaro.

A cikin ’yan watannin nan ’yan ta’adda a hare-harensu, suka kashe wani Janar din soja, Kwamandan Birget na 25 da ke Jihar Borno, Birgediya-Janar Uba Musa da dakarunsa a Jihar Borno, inda kuma suka yi garkuwa da wasu mata a gona.

A kwanan nan ’yan ta’adda sun tsananta kai hare-hare a Jihar Kano, baya ga sace daruruwan dalibai a jihohin Kebbi da Neja da kuma yin garkuwa da masu ibada a Jihohin Kwara da Kogi da kuma sace wasu mata a Borno.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka za ta hana ’yan Najeriyar da ake zargi da yi wa Kiristoci kisan kiyashi biza
  • NAJERIYA A YAU: Abun Da Masu Ruwa Da Tsaki Ke Yi Na Dakile Laifuka A Wurin Matasa
  • ’Yan Najeriya suna da ƙwarin guiwa a kaina, ba zan ba su kunya ba — Ministan Tsaro
  • Tsaro: Gwamnatin Kano za ta fara amfani da jirage marasa matuƙa a iyakokinta
  • CBN ya kara yawan kudin da mutum zai iya cirewa a mako zuwa N500,000
  • DAGA LARABA: Kalubalen Dake Gaban Janar Christopher Musa A Matsayin Ministan Tsaro
  • NAJERIYA A YAU: Matsalar Kansar Mama Da Hanyoyin Magance Shi
  • Jagoran ‘Yan Democrat a Majalisar Dattawa: Trump Ba Shi da Ikon Kaddamar da Yaki Kan Venezuela
  • Tinubu ya gana da Janar Christopher Musa bayan Ministan Tsaro ya yi murabus
  • Sarkin Musulmi ya buƙaci gwamnonin Arewa suke saurarar ƙorafin jama’a