Jakadan Amurka Ya Ziyarci Sarkin Zazzau Domin Karfafa Alakar Amurka Da Najeriya
Published: 20th, March 2025 GMT
Jakadan Amurka a Najeriya, Richard Mills Jr, ya ziyarci mai martaba Sarkin Zazzau Malam Ahmad Bamalli domin ingantawa da karfafa hadin kan al’adu.
Jekadan ya ce Amurka ta jajirce sosai kan alakar da Najeriya ya kara da cewa; ‘ muna so mu zurfafa shi kuma mu ƙarfafa shi.”
A cewarsa, hanyar da ta fi dacewa wajen zurfafa wannan alaka ita ce ta haduwa irin wannan da za mu ji ta bakin juna.
“Ina sa ran jin ta bakinku kan abubuwan da kuke yi na karfafa hadin kan addini a tsakanin al’umma, damar ilimi da kuma damar yin aiki ga jama’ar ku.
“Abin da Amurka za ta iya yi don haɓaka ƙarin alaƙa da kuma matakan da za mu iya ɗauka don zurfafa dangantakarmu,” in ji Mills.
Da yake mayar da jawabi, Mai martaba Sarkin Zazzau ya yabawa ma’aikatar harkokin wajen Amurka kan bude cibiyar kula da harkokin a Amurka a jami’ar Ahmadu Bello.
Bamalli ya yi fatan wannan cibiar da aka kira da Window on America da turanci ta zama matakin samar da ingantacciyar dama tsakanin Amurka da masarautar Zazzau da jihar Kaduna.
Ya kara da cewa masarautar na da alaka mai tsawo da ofishin jakadancin Amurka inda ya kara da cewa tawagogin ofishin jakadanci sun kasance suna halartar Dabar karshen watan Ramadan a Zariya.
“Amma hakan ya tsaya cik tsawon wasu shekaru saboda rashin tsaro, amma za mu iya cewa zaman lafiya ya dawo ga al’ummarmu.
“Saboda haka, muna fatan mambobin ofishin jakadancin da sauran jami’an diflomasiyya za su ci gaba da halartar bukukuwan Sallah Durbar,” in ji Bamalli.
COV/ Ibrahim Suleiman
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Nijeriya
এছাড়াও পড়ুন:
HKI Ta Kashe Falasdianwa 6 A Gaza, Kuma Tsoffin Fursinoni
Wani babban jami’I a kungiyar Hamas ya bayyana cewa sojojin HKI sun kashe falasdinawa guda 6 a zirin gaza a ci gaba kissan kiyashin da takewa falasdinawa a yankin.
Abdul-Karim Hanini, ya kara da cewa wadanda ta kashen tsoffin fursinoni a hannun yahudawan a shekarun da suka gaba 5 daga cikinsu an yi musayarsu ne a shekara 2011 a lokacinda aka yi musayarsu da fursinan yahudawan Galid Shalit a shekarar. Sannan dayan kuma an yi musayarsa ne a shekara ta 2002 wanda yahudawan suka kora daga Cocin Nativity daga birnin Bethlaham a yankin yamma da kogin Jordan.
Abdul-Karim Hanini ya kammala da cewa a dai dai lokacinda muke makokin yan’uwammu da yahudawan suka kai ga shahata, muna rokon All..ya karbi shahadarsu, sannan muna kara nanata cewa zamu ci gaba da gwagwarmaya da su har zuwa jinni na karshe da zamu iya zubarwa ko kuma mu sami nasara a kansu.