Jakadan Amurka a Najeriya, Richard Mills Jr, ya ziyarci mai martaba Sarkin Zazzau Malam Ahmad Bamalli domin ingantawa da karfafa hadin kan al’adu.

 

Jekadan ya ce Amurka ta jajirce sosai kan alakar da Najeriya ya kara da cewa; ‘ muna so mu zurfafa shi kuma mu ƙarfafa shi.”

 

A cewarsa, hanyar da ta fi dacewa wajen zurfafa wannan alaka ita ce ta haduwa irin wannan da za mu ji ta bakin juna.

 

“Ina sa ran jin ta bakinku kan abubuwan da kuke yi na karfafa hadin kan addini a tsakanin al’umma, damar ilimi da kuma damar yin aiki ga jama’ar ku.

 

“Abin da Amurka za ta iya yi don haɓaka ƙarin alaƙa da kuma matakan da za mu iya ɗauka don zurfafa dangantakarmu,” in ji Mills.

 

Da yake mayar da jawabi, Mai martaba Sarkin Zazzau ya yabawa ma’aikatar harkokin wajen Amurka kan bude cibiyar kula da harkokin a Amurka a jami’ar Ahmadu Bello.

 

Bamalli ya yi fatan wannan cibiar da aka kira da Window on America da turanci ta zama matakin samar da ingantacciyar dama tsakanin Amurka da masarautar Zazzau da jihar Kaduna.

 

Ya kara da cewa masarautar na da alaka mai tsawo da ofishin jakadancin Amurka inda ya kara da cewa tawagogin ofishin jakadanci sun kasance suna halartar Dabar karshen watan Ramadan a Zariya.

 

“Amma hakan ya tsaya cik tsawon wasu shekaru saboda rashin tsaro, amma za mu iya cewa zaman lafiya ya dawo ga al’ummarmu.

 

“Saboda haka, muna fatan mambobin ofishin jakadancin da sauran jami’an diflomasiyya za su ci gaba da halartar bukukuwan Sallah Durbar,” in ji Bamalli.

 

COV/ Ibrahim Suleiman

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Wike: Za mu kare duk wani soja da ke aiki bisa doka — Ministan Tsaro

Ministan Tsaro, Mohammed Badaru, ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya tare da shugabannin Rundunonin Sojin Najeriya, za su ci gaba da kare duk wani jami’i da ke gudanar da aikinsa bisa doka.

Badaru, ya bayyana hakan ne lokacin da yake ganawa da manema labarai a taron da aka shirya domin bikin tunawa da Sojojin Najeriya na shekarar 2026 a Abuja.

’Yan sanda sun kama mutum 14 kan zargin ta’amali da miyagun ƙwayoyi a Jigawa MDD ta sanya Najeriya cikin ƙasashe 16 da ke fama da tsananin yunwa

Wannan na zuwa ne bayan ce-ce-ku-cen da ya faru ranar Talata tsakanin Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, da wani jami’in rundunar sojan ruwa, Laftanar A. M. Yerima.

An yi taƙaddama ne kan wani fili da ke Abuja da ake zargin mallakar wani tsohon Shugaban Rundunar Sojin Ruwa, Vice Admiral Awwal Gambo (mai ritaya) ne.

“A Ma’aikatar Tsaro, da kuma rundunonin sojoji, za mu ci gaba da kare jami’anmu masu aiki bisa doka,” in ji Badaru.

“Muna binciken al’amarin da ya faru, kuma muna tabbatar da cewa duk wani jami’i da yake aikinsa yadda doka ta tanada za a kare shi. Ba za mu bari wani abu ya same shi ba matuƙar yana yin aikinsa da kyau.”

Ministan, ya kuma sanar da sabon shirin gwamnati na haɗa tsofaffin sojoji cikin aikin tsaron al’umma da ci gaban yankuna ta hanyar shirin “Reclaiming the Ungoverned Space for Economic Benefits Programme (RUSEB-P)”.

Ya ce manufar shirin ita ce amfani da ƙwarewar tsofaffin jami’an tsaro domin tabbatar da zaman lafiya da ci gaba a yankunan da ake samun rikice-rikice.

Badaru, ya bayyana cewa shirin RUSEB-P zai taimaka wajen rage aukuwar ta’addanci da kuma bunƙasa harkokin noma, hakar ma’adinai, da sauran ayyukan tattalin arziƙi.

Ya ƙara da cewa an kafa kwamiti da ke aiki kan yadda za a aiwatar da shirin.

Haka kuma, ya bayyana cewa gwamnati na shirin sake duba ‘Nigerian Legion Act’ domin kafa Ƙungiyar Tsofaffin Sojojin Najeriya (Veterans Federation of Nigeria – VFN), wacce za ta ƙarfafa tsarin kariya da tallafa wa walwalar tsofaffin jami’an tsaro.

Ya tabbatar da cewa Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da aiwatar da sauye-sauye da za su inganta tsaron ƙasa, inganta walwalar sojoji, da kuma girmama sadaukarwar tsofaffin jami’an tsaro.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • MURIC ta buƙaci Tinubu ya sauke Amupitan daga shugabancin INEC
  • Wike: Za mu kare duk wani soja da ke aiki bisa doka — Ministan Tsaro
  • MDD ta sanya Najeriya cikin ƙasashe 16 da ke fama da tsananin yunwa
  • Jihar Jigawa Za ta Kashe Sama da Naira Biliyan Daya Domin Inganta Ayyukan Wutar Lantarki
  • DSS ta gurfanar da matashin da ya yi kira a yi juyin mulki a Najeriya a gaban kotu
  • AIG Zubairu Ya Umurci ‘Yan Sanda a Kwara Su Ninka Kokarinsu Don Karfafa Tsaro
  • Araghchi: Matsalar Yammacin duniya ita ce ci gaban kimiyyar Iran ba makaman nukiliya ba
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Malaman Jami’oi Masu Zaman Kansu Na Shiga Kungiyar ASUU
  • Sarkin Musulmi ya ba wa makarantu tallafin N1.3bn a Kebbi
  • APC Ta Yi Gangamin Karfafa Hadin Kan Mambobinta Bayan Kaddamar Da Aikin Titin Malam Madori