A ranar 19 ga watan Maris na ko wace shekara ne mutanen Iran suke gudanar da bukukuwan tunawa da ranar da mutanen kasar tare da taimakon gwamnatin lokacin suka sami nasarar kwace kamfanin haka da sarrafa man fetur na kasar, daga hannun wani kamfanin mai na kasar Burtaniya suka maida shin a kasa.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya ce , wannan rana abin alfakhari ne ga mutanen kasar, don bayan haka ne kasar ta sami ikon kawo ci gaban tattalin arzikin kasar da kuma shimfida harsashen samun yencin kasar daga hannun kasashen yamma wadanda suka mamaye bangarori da dama a cikin al-amuran kasar.

A ranar 19 ga watan Maris na shekara ta 1951 ne, wato shekaru 78 da suka gabata,  firai ministan kasar Iran na lokacin Dr Muhammad Musaddiq tare da taimakon malaman addini ya sami nasarar kwace kamfanin man fetur na kasar daga hannun turawan ingila ya maida shi na kasa.

Majalisar dokokin kasar Iran ta amince da dokar maida kamfanin ya zama ta kasa a ranar 17 ga watan Maris na shekara ta 1951, sannan majalisar dattawan kasar ta amince da Ita a ranar 19 ga watan Maris na shekarar.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: ga watan Maris na

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya ta yi jimami kan mutuwar mutanen da suka rasu a fashewar motar mai a Jihar Neja

Gwamnatin Tarayya ta bayyana alhinin ta kan mummunar haɗarin fashewar motar mai da ta faru a ƙauyen Essa, cikin Karamar Hukumar Katcha ta Jihar Neja, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da dama tare da jikkata wasu da yawa.

 

A cikin wata sanarwa da Ministan Yada Labarai da Tsarin Ƙasa, Mohammed Idris, ya sanya wa hannu, Gwamnatin Tarayya ta yi ta’aziyya ga Gwamnatin Jihar Neja da al’ummar jihar bisa wannan babban rashi, tana mai bayyana lamarin a matsayin abin tunawa da illar da ke tattare da haɗarin motocin mai a ƙasar.

 

Sanarwar ta nuna damuwa kan yadda, duk da wayar da kai da gargadin da ake yi a kai a kai, wasu ’yan ƙasa har yanzu ke shiga cikin haɗari ta hanyar kwasar mai daga motoci da suka kife, wanda hakan kan haifar da asarar rayuka da dukiya.

 

Ministan ya jaddada cewa duk rayuwar ɗan Najeriya tana da muhimmanci, tare da yin kira da a ƙara lura da bin matakan tsaro a lokutan gaggawa.

 

Ya yaba wa Gwamnatin Jihar Neja, jami’an tsaro, da kuma masu aikin ceto bisa saurin da suka nuna wajen kashe wutar da kuma ceto rayuka.

 

Haka kuma, Ministan ya bayyana cewa Hukumar Kula da Bala’o’i ta Ƙasa (NEMA) ta samu umarni da ta ci gaba da ba da tallafi da taimakon gaggawa ga waɗanda abin ya shafa, yayin da Hukumar Wayar da Kan Jama’a (NOA) za ta ƙara ƙaimi wajen yaɗa faɗakarwa domin hana irin wannan bala’i a nan gaba.

 

Gwamnatin Tarayya ta miƙa ta’aziyyarta ga iyalan waɗanda suka mutu, tare da yin addu’a ga Allah Ya jikansu, Ya kuma ba waɗanda suka jikkata lafiya ta ƙwarai.

 

Bello Wakili

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing
  • Kasar Sin Ta Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Na 15
  • Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria
  • Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa
  • Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 
  • Gombe Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Rano Air Don Fara Jigila Tsakanin Abuja Zuwa Gombe
  • Shugaban Kasar Sin Zai Halarci Taron APEC Da Ziyarar Aiki A Korea Ta Kudu
  • Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba
  • Gwamnatin Tarayya ta yi jimami kan mutuwar mutanen da suka rasu a fashewar motar mai a Jihar Neja