A Jiya Laraba Ce Iran Take Bukukuwan Cika Shekaru 78 Da Kwatar Kamfanin Man Fetur Na Kasar Daga Hannun Turawan Burtaniya
Published: 20th, March 2025 GMT
A ranar 19 ga watan Maris na ko wace shekara ne mutanen Iran suke gudanar da bukukuwan tunawa da ranar da mutanen kasar tare da taimakon gwamnatin lokacin suka sami nasarar kwace kamfanin haka da sarrafa man fetur na kasar, daga hannun wani kamfanin mai na kasar Burtaniya suka maida shin a kasa.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya ce , wannan rana abin alfakhari ne ga mutanen kasar, don bayan haka ne kasar ta sami ikon kawo ci gaban tattalin arzikin kasar da kuma shimfida harsashen samun yencin kasar daga hannun kasashen yamma wadanda suka mamaye bangarori da dama a cikin al-amuran kasar.
A ranar 19 ga watan Maris na shekara ta 1951 ne, wato shekaru 78 da suka gabata, firai ministan kasar Iran na lokacin Dr Muhammad Musaddiq tare da taimakon malaman addini ya sami nasarar kwace kamfanin man fetur na kasar daga hannun turawan ingila ya maida shi na kasa.
Majalisar dokokin kasar Iran ta amince da dokar maida kamfanin ya zama ta kasa a ranar 17 ga watan Maris na shekara ta 1951, sannan majalisar dattawan kasar ta amince da Ita a ranar 19 ga watan Maris na shekarar.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: ga watan Maris na
এছাড়াও পড়ুন:
Katafaren Jirgin Daukar Jiragen Yaki Na Kasar Amurka Harry Truman Zai Fice Daga Tekun Maliya
Rahotannin da suke fitowa daga kasar Yemen na cewa katafaren jirgin ruwa mai daukar jiragen saman yaki malakar klasarAmurka wato USS Harry Truman zai fice daga tekun red sea da nan kusa saboda makaman kasar Yemen da suka fada mata.
Tashar talabijin ta Almasirah ta kasar Yemen ta nakalto wani jami’in ma’aikatar tsaron kasar wanda baya son a bayyana sunansa yana cewa, saboda yawan hare haren da sojojin Yemen suka kaiwa jirgin, wadanda suka hada da amfani da makamai masu linzami samfurin Crusse da kuma Balistic, har ila yau da jiragen yaki masu kunan bakin waken da suka fada a kansa. A yanzun ya zama dole jirgin ya fice daga tekun.
Tun cikin watan Maris da ya gabata ne gwamnatin shugaba Trump ta fara kaiwa kasar yemen hare-hare da jiragen sama wadanda suke tashi daga sansanin jiragen yaki da ke kan wannan jirgin. Saboda tilastawa kasar Yemen dakatar da kai hare-hare a kan HKI, don ta kawo karshen tallafawa Falasdinawa a Gaza.
Amma ya zuwa yanzu hare-haren na Amurka sun kasa kaiwa ga bukata, majiyar gwamnatin kasar ta yemen ta ce hare-haren Amurka a kasar ba zasu sa ta dakatar da tallafawa Falasdinawa, da kuma hanata kai hare hare kan jiragen kasuwanci na HKI masu wucewa ta tekun red sea ba.
A wani labarin kuma hare haren na sojojin yemen sun sa wani jiegin yakin Amurka samfurin F-18 ya fada cikin ruwa a tekun na Red Sea a kokarin kaucewa makaman sojojin Yemen.