A ranar 19 ga watan Maris na ko wace shekara ne mutanen Iran suke gudanar da bukukuwan tunawa da ranar da mutanen kasar tare da taimakon gwamnatin lokacin suka sami nasarar kwace kamfanin haka da sarrafa man fetur na kasar, daga hannun wani kamfanin mai na kasar Burtaniya suka maida shin a kasa.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya ce , wannan rana abin alfakhari ne ga mutanen kasar, don bayan haka ne kasar ta sami ikon kawo ci gaban tattalin arzikin kasar da kuma shimfida harsashen samun yencin kasar daga hannun kasashen yamma wadanda suka mamaye bangarori da dama a cikin al-amuran kasar.

A ranar 19 ga watan Maris na shekara ta 1951 ne, wato shekaru 78 da suka gabata,  firai ministan kasar Iran na lokacin Dr Muhammad Musaddiq tare da taimakon malaman addini ya sami nasarar kwace kamfanin man fetur na kasar daga hannun turawan ingila ya maida shi na kasa.

Majalisar dokokin kasar Iran ta amince da dokar maida kamfanin ya zama ta kasa a ranar 17 ga watan Maris na shekara ta 1951, sannan majalisar dattawan kasar ta amince da Ita a ranar 19 ga watan Maris na shekarar.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: ga watan Maris na

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Siyasa Ne Ke Zagon Ƙasa Ga Ci Gaban Nijeriya — Sarki Sanusi II

Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya zargi ‘yan siyasan Nijeriya da zagon kasa ga ci gaban kasar ta hanyar daukar mukaman gwamnati a matsayin gadon gidansu a maimakon amanar jama’a. Da yake jawabi a ranar Laraba a yayin taro karo na 15 mai taken, “ya Isa haka” da ya gudana a jihar Legas, Sanusi II ya ce manyan ‘yan siyasa a fadin Nijeriya, suna ci gaba da yin zagon kasa ga ci gaban kasa saboda suna fifita kansu, iyalansu da abokan huldarsu fiye da kasar da ‘yan kasarta. Nazarin CGTN: Fahimtar Matsayin Sin Cikin Yanayin Tattalin Arzikin Duniya Na Da Muhimmanci Katsina Ta Amince Da Bayar Da Alawus Na Naira 30,000 Duk Wata Ga Malaman Karkara Ya yi takaicin cewa, gazawar Nijeriya a wasu wurare ba haka nan take ba, face sakamakon shugabanci na son kai. A cewarsa, “mukaman gwamnati na su ne, da iyalansu, da mutanen da ke kusa da su, babu ruwansu da ‘yan kasar. Amma mukaman gwamnati na ‘yan kasa ne.” Sarki Sanusi na II ya yi kira ga matasan Nijeriya da su yi watsi da tsarin da ‘yan siyasa marasa kishin kasa suka kafa na amfani da “kabilanci, rikice-rikicen addini, da kuma son kai,” a maimakon haka, su hada kai don gina kasa da za ta cika mafarkanta. Ya jaddada cewa, ikon kasa yana hannun ‘yan kasa ne, ba ‘yan siyasa ba, ya kara da cewa, kowane mutum yana da rawar da zai taka a hakkinsa don tallafawa Nijeriya. ADVERTISEMENT ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Kotu Ta Yanke Wa Wani Mutum Hukuncin Kisa Bisa Garkuwa Da Kashe Mai Gidansa A Kano December 11, 2025 Labarai Mahajjata 2,235 Ne Suka Yi Rijistar Aikin Hajjin 2026 A Sokoto December 11, 2025 Manyan Labarai Katsina Ta Amince Da Bayar Da Alawus Na Naira 30,000 Duk Wata Ga Malaman Karkara December 11, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaba Tinubu Ya Karrama Shugaban NPA Da Lambar Yabo Ta Musamman
  • Duniyarmu A Yau: Iran Da Amurka A Yakin Kwanaki 12 Wa Ya Sami Nasara
  • Za A Yi Manyan Zabuka A Kasar Habasha A Watan Yuni Na 2026
  • Kamfanin CRCC Ya Kammala Shimfida Hanyar Jirgin Kasa A Gadar Layin Dogo Mafi Tsawo A Afrika Dake Algeria
  • Yadda Bunkasar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samar Da Karin Damammaki Ga Kasashe Masu Tasowa
  • ‘Yan Siyasa Ne Ke Zagon Ƙasa Ga Ci Gaban Nijeriya — Sarki Sanusi II
  • BUA ya tallafa wa ɗaliban Sakkwato 200 da miliyan 40
  • Iran da Kazakhstan Sun rattaba hannun kan yarjeniyoyi da dama a tsakaninsu
  • Zanga-zanga ta ɓarke bayan haɗarin tirela ta kashe mutum a Yobe
  • Shugaban Kasar Iran Yace Mata Su ne Ginshin Gina Makomakar Kowacce Kasa