Aminiya:
2025-06-14@01:30:49 GMT

Motar da aka shekara 10 ana tara kuɗinta ta ƙone bayan awa 1 da sayen ta

Published: 18th, May 2025 GMT

Bayan da wani matashi ɗan shekara 33 ɗan kasar Japan mai suna Honkon ya yi tarin kuɗi na tsawon shekaru 10 don siyan motar da yake mafarki — na wata sabuwar mota ƙirar Ferrari 458 Spider — sai ya zauna yana kallon yadda motar take ƙonewa cikin sa’a ɗaya da tuƙa ta a karon farko.

Kafofin sada zumunta na ƙasar Japan sun yi sharhi game da rahoton baƙin ciki na Honkon, matashin da ya kasance mai shirya wakoki, wanda ya kashe makudan kuɗi game da mafarkin sayan motarsa ta Ferrari, sai dai ya kalle ta tana ci da wuta a ranar da ya tuƙa ta a karon farko.

ISWAP ta kashe manoma sama da 50 a Borno Guguwar raba Masarautar Katsina ta kunno kai

Dan shekara 33 kwanan nan ya dauki hankalin mabiya manhajar X (Twitter) don yaɗa labarin kan yadda zai ji daɗin gaskata mafarkin mallakar Ferrari a ’yan mintuna kaɗan kawai ta kama da wuta yayin da yake tuƙi a kan babbar titin Shuto a Tokyo, Laraba, 16 ga Afrilu.

A bayyane yake, an kawo masa zabinsa Spider 458 ne kawai, kuma yana cikin motar kan gwaji tare da shi lokacin da ya lura da fitar wani farin hayaki.

Da farko ya ɗauka hayakin daga motar da ke kusa da tasa motar yake fita, amma yayin da motar ta yi gaba, sai ga shi hayakin yana fitowa daga cikin motar Ferrari.

Don haka sai kawai Honkon ya janye, ya fita daga cikin motar, ya kira hukumar kashe gobara.

Ya kwashe mintuna 20 yana kallon burinsa ta ƙone kusan gaba ɗaya.

“Ina tsammanin ni kadai ne mutum a Japan da ya taba fuskantar irin wannan matsala,” Honkon ya rubuta a shafin X, tare da taken hoton motar da ke konewa.

“Na kashe yen miliyan 43 kwatankwacin (Naira miliyan dari 4 da miliyan 92 dubu dari 283 da 620), kuma abin da na samu shi ne wannan hoton.”

Rundunar ’yan sandan birnin Tokyo ta sanar da cewa, babu alamun karo a jikin motar Honkon ta Ferrari, amma ana ci gaba da gudanar da bincike.

An yi imanin cewa gobarar ta tashi ne a cikin injin motar, amma har yanzu ba a san dalilin ba.

Yayin da a fili yake matashin ya yi bakin cikin rashin motarsa, Honkon ya shaida wa mabiyansa cewa ya yi farin ciki da ya rayu, domin yana tsoron cewa motar za ta iya fashewa yana ciki.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Iran ta caccaki kudurin IAEA wanda ta ce yana cike da siyasa

Iran ta yi Allah-wadai da wani kuduri da ta danganta da na siyasa da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA ta dauka, tana mai cewa ba shi da tushe na fasaha ko doka.

Hukumar kula da makamashin nukiliya ta Iran (AEOI) da ma’aikatar harkokin wajen kasar sun fitar da sanarwar hadin gwiwa yau Alhamis bayan da majalisar gwamnonin hukumar ta IAEA suka amince da wani kuduri da ke zargin Iran da rashin cika alkawuran da ta dauka na nukiliya.

Kuri’u 19 ne suka amince da kudurin wanda Amurka da Birtaniya da Faransa da Jamus suka tsara.

Kasashen Rasha, China da Burkina Faso sun kada kuri’ar kin amincewa da shi, Yayin da kasashen Afirka ta Kudu, Indiya, Pakistan, Masar, Indonesia da Brazil suka ce su kam ba ruwan su.

Sanarwar da Iran ta fitar dangane da wannan kudiri ta ce, Jamhuriyar Musulunci ba ta da wani zabi face mayar da martani ga wannan kudiri na siyasa.”

Sanarwar ta ce, Shugaban Hukumar Makamashin Nukiliya ta Iran (AEOI), Mohammad Eslami, ya ba da umarnin gina sabuwar cibiyar tace uranium a wani wuri mai aminci.

Sabuwar cibiyar za ta kunshi sabbin na’urorin tace uranium na zamani inji sanarwar.

A cikin sanarwar, Tehran ta yi tir da kudirin na “siyasa da son zuciya” na IAEA  Wanda Amurka da manyan kasashen Turai uku – Faransa, Jamus da Birtaniya suka tsara.

Iran ta kuma yi tir da shirun da Amurka da kawayenta na Turai suka yi wajen tinkarar yadda gwamnatin Isra’ila ke ci gaba da kin mutunta yarjejeniyar hana yaduwar makaman kare dangi.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da Iran da Amurka suka tabbatar da sake ganawa a karo na shida a ranar Lahadi mai zuwa game da shirin nukiliyar Iran wanda a’a gudanar a birnin Muscat a shiga stakanin kasar Oman.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwamadan Sararin Samaniyar Iran Na Dakarun Kare Juyi Haji Zadeh Yana Cikin Wadanda Su Ka Yi Shahada
  • Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — Dalung
  • Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje
  • Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna
  • Iran ta caccaki kudurin IAEA wanda ta ce yana cike da siyasa
  • Gobara Ta Ƙone Wani Gidan Mai A Legas
  • Ministan Tsaro Na Kasar Iran ya bada Labarin Gwajin Wani Sabom Makami Mai Limzami Mai Daukar abubuwan Fashewa Har Ton Biyu
  • Gini ya kashe Ba’indiye a Zariya
  • ‘Yan Bindiga Sun Sake Kashe Mutane 8 A Jihar Filato
  • Na shirya yin haɗaka don ƙalubalantar Tinubu a 2027 – Amaechi