Motar da aka shekara 10 ana tara kuɗinta ta ƙone bayan awa 1 da sayen ta
Published: 18th, May 2025 GMT
Bayan da wani matashi ɗan shekara 33 ɗan kasar Japan mai suna Honkon ya yi tarin kuɗi na tsawon shekaru 10 don siyan motar da yake mafarki — na wata sabuwar mota ƙirar Ferrari 458 Spider — sai ya zauna yana kallon yadda motar take ƙonewa cikin sa’a ɗaya da tuƙa ta a karon farko.
Kafofin sada zumunta na ƙasar Japan sun yi sharhi game da rahoton baƙin ciki na Honkon, matashin da ya kasance mai shirya wakoki, wanda ya kashe makudan kuɗi game da mafarkin sayan motarsa ta Ferrari, sai dai ya kalle ta tana ci da wuta a ranar da ya tuƙa ta a karon farko.
Dan shekara 33 kwanan nan ya dauki hankalin mabiya manhajar X (Twitter) don yaɗa labarin kan yadda zai ji daɗin gaskata mafarkin mallakar Ferrari a ’yan mintuna kaɗan kawai ta kama da wuta yayin da yake tuƙi a kan babbar titin Shuto a Tokyo, Laraba, 16 ga Afrilu.
A bayyane yake, an kawo masa zabinsa Spider 458 ne kawai, kuma yana cikin motar kan gwaji tare da shi lokacin da ya lura da fitar wani farin hayaki.
Da farko ya ɗauka hayakin daga motar da ke kusa da tasa motar yake fita, amma yayin da motar ta yi gaba, sai ga shi hayakin yana fitowa daga cikin motar Ferrari.
Don haka sai kawai Honkon ya janye, ya fita daga cikin motar, ya kira hukumar kashe gobara.
Ya kwashe mintuna 20 yana kallon burinsa ta ƙone kusan gaba ɗaya.
“Ina tsammanin ni kadai ne mutum a Japan da ya taba fuskantar irin wannan matsala,” Honkon ya rubuta a shafin X, tare da taken hoton motar da ke konewa.
“Na kashe yen miliyan 43 kwatankwacin (Naira miliyan dari 4 da miliyan 92 dubu dari 283 da 620), kuma abin da na samu shi ne wannan hoton.”
Rundunar ’yan sandan birnin Tokyo ta sanar da cewa, babu alamun karo a jikin motar Honkon ta Ferrari, amma ana ci gaba da gudanar da bincike.
An yi imanin cewa gobarar ta tashi ne a cikin injin motar, amma har yanzu ba a san dalilin ba.
Yayin da a fili yake matashin ya yi bakin cikin rashin motarsa, Honkon ya shaida wa mabiyansa cewa ya yi farin ciki da ya rayu, domin yana tsoron cewa motar za ta iya fashewa yana ciki.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Abbas Arakci Ya Yi Gargadi Akan Abin Zai Biyo Bayan Keta Dokokin Duniya Da “Isra’ila” Take Yi A Cikin Wannan Yankin
Ministan harkokin wajen na Jamhuriyar Musulunci ta Iran Abbas Arakci wanda yake ziyarar aiki a kasar Oman ya gana da manzon musamman na MDD a kasar Yemen Hans Grundberg a jiya Litinin ya yi tir da yadda Haramtacciyar Kasar Isra’ila take keta dokoki tana kai wa kasashen wannan yankin hare-hare.
Haka nan kuma ministan harkokin wajen na Iran ya kuma nuna kin amincewar jamhuyriyar musulunci ta Iran da yadda ake ci gaba da killace kasar Yemen, yana mai yin gargadi akan sakamakon da zai biyo bayan keta doka da ‘yan Sahayoniya suke yi da shi ne ci gaba da hargitsi da fadace-fadace a wannan yankin.
A nashi gefen manzon musamman na MDD a kasar Yemen ya bukaci ganin Iran ta ci gaba da bai wa Majalisar Dinkin Duniyar hadin kai domin kyautata rayuwar al’ummar kasar ta Yemen da kuma shimfida zaman lafiya.
A wani labari mai alaka da ma’aikatar harkokin wajen Iran ta amabci cewa za a yi ganawa a tsakanin minista Abbas Arakci da takwaransa na Faransa Jean Noel Baro a gobe Laraba 26/ Nuwamba a birnin Paris.
Jigon tattaunawar shi ne bunkasa alaka a tsakanin kasashen biyu da kuma batun furusunonin Faransa da suke a Iran.
Haka nan kuma tattaunawar bangarorin biyu za ta tabo halin da ake ciki a wannan yankin na yammacin Asiya, sai kuma Shirin Iran na makamashin Nukiliya.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka An Gudanar Da Jana’izar Shahidai 300 A Dai-Dai Ranar Shahadar Zahra (s) A Jiya Litinin November 25, 2025 Amurka Da HKI Sun Kawo Karshen Hukumar GHF Mai Raba Abinci A Gaza November 25, 2025 Babban Kwamandan Sojojin Sudan Ya Yi Watsi Da Shirin Trump Na Zaman Lafiya November 25, 2025 Hamas Ta Ce Keta Hurumin Tsagaita Wutan Da HKI Take Yi Zai Iya Kawo Karshen Tsagaita Wutar November 25, 2025 Gwamnonin Kudu Maso Yammacin Najeriya Sun Ce Lokacin Kafa Yansandan Jihohi Ya Yi November 25, 2025 Hizbullah Ta na Juyayin shahadar Babban Kwamanda Haitham Ali Da Isra’ila Ta Kashe. November 24, 2025 Dubban Alummar Kasar Tunisia Ne Suka Gudanar Da Zanga-zangar Adawa Da Mulkin Kama Karya A Kasar November 24, 2025 Mutane 6 Ne Suka Mutu Sakamakon Harin Kunar Bakin Wake Da Aka Kai A Peshavar Na Kasar Pakistan November 24, 2025 Hamas Tayi Gargadi Game Da Rushewar Yarjejeniyar Bude Wuta Idan Israila Ta ci Gaba Da Kai Hare-Hare November 24, 2025 Amnesty International Ta Zargi Najeriya Da Gazawa Wajen Kare Rayukan Al’ummarta November 24, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci