Leadership News Hausa:
2025-07-03@09:43:47 GMT

‘Yan Kasuwa 27 Sun Rasu A Wani Hatsarin Kwale-kwale A Kwara

Published: 18th, May 2025 GMT

‘Yan Kasuwa 27 Sun Rasu A Wani Hatsarin Kwale-kwale A Kwara

Shugaban karamar hukumar Kaiama, Honarabul Abdullah Danladi ya tabbatar da afkuwar lamarin a ranar Lahadi yayin wata tattaunawa da LEADERSHIP ta wayar tarho.

 

Danladi ya ce ya jagoranci tawagar gwamnati domin jajantawa iyalan wadanda abin ya shafa.

 

Ya kara da cewa, gwamnati za ta kafa wani kwamiti wanda za a dora masa alhakin tilasta wa fasinjojin jirgin ruwa yin amfani da rigar tsira don dole.

 

Danladi ya ce gwamnati za ta kuma dakatar da tafiye-tafiye da daddare a wani bangare na matakan kawo karshen yawaitar haduran Kwale-kwale da ake fama da shi a yankunan da ke zagaye da ruwa.

 

Shi ma mai martaba Sarkin Kaiama, Alh Muazu Omar ya nuna alhininsa kan wannan lamari da ya faru.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Lebanon Ta Nuna Damuwarta Da Yiyuwar Yan Ta’adda Daga Siriya Su Kawo Hare-Hare Cikin Kasar

Bayan hare-haren da kungiyoyin yan ta’adda masu iko da kasar Siriya suka kai kan wani Cuci a kasar Siriya jami’an gwamnatin kasar Siriya sun nuna damuwarsu da yiyuwar wadannan kungiyoyi su kawo hare-hare a cikin kasar ta Lebanon musamman a cikin wadan nan kwanaki na makokin Imam Hussain (a).

Wani Jami’in gwamnati a kasar ta Lebanon ya fadawa Jaridar da The National ta kasar Amurka kan cewa a makon da ya gabata an kama wani shugaban yan kungiyar yan ta’adda ta ISIS a cikin kasar, tare da zarginsa da shiri hare-hare masu yawa a kasar Lebanon.

Kafin haka dai a cikin watan da ya gabata wani dan ta’ada ya tarwatsa kansa a cikin wani coci a birnin Damascus babban birnin kasar Siriya inda ya kashe mutane 25.

Kungiyar yan ta’adda ta Daesh dai sun fara aiki karkashin kasa tun bayan da dakarun kungiyar Hizbulla.. da kuma sojojin kasar Lebanon sun fatattakesu a shekara 2017. Sannan a wasu lokutan sun kai hare-hare kan kungiyar Hizbullah a kasar.

Sannan bayan kungiyar HTS ta kwace mulki a hannun shugaba Asad a shekarar da ta gabata, har yanzun akwai yiyuwar barazanar hare-haren ISIS tana nan a kan kasar ta Lebanon.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ɗan wasan Liverpool, Diogo Jota, ya mutu a hatsarin mota
  • Hukumar Makamashin Nukiliya Ta Iran Ta Bayyana Lokacin Ci Gaba Da Ayyukan Cibiyoyinta Ta Nukiliya
  • ’Yan sanda sun kama wani mutum da jabun kuɗi a Gombe
  • Majalisar Dokokin Filato ta zaɓi sabon shugaba
  • Wargajewar HKI Ba Makawa Inji Wani Janar Daga Sojojin JMI
  • Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano
  • Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara
  • Magidanci ya kashe matarsa da adda a Yobe
  • Lebanon Ta Nuna Damuwarta Da Yiyuwar Yan Ta’adda Daga Siriya Su Kawo Hare-Hare Cikin Kasar
  • ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4