Mutane Fiye Da 30 Ne Suka Rasa Rayukansu A Lokacinda Motar Dawkar Gas Ta Yi Bindiga A Abuja Na Tarayyar Najeriya
Published: 20th, March 2025 GMT
Mutane fiye da 30 ne aka tabbatar damutuwarsu a jiya Laraba a Abubja babban birnin tarayyar Najeriya sanadiyyar bindigan da wata motar daukar iskar gas ta yi a kan gadar Karo da misalign karfe 7:15 a jiya Laraba.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa hatsarin na jiya ya aukune a dai dai lokacinda direba wata motar dakon mai ta Burma kan wasu ababen hawa a kan gadar Karu dake kan hanyar Abuja-Keffi, sannan ta yi bindiga wanda ya tarwatsa wuta kan motocin da ta tsarewa hanya da dama daga cikin motocin su kuma da wuta kuma mazauna cikinsu sun kasa fita.
Ya zuwa yanzu dai jami’an kwana-kwana da kuma majiyar asbitoci a Asokoro da Asbitin kasa sun tabbatar da mutuwar fiye da 30 sannan wasu da dama suna jinya.
Bayan bayan hawa shugaba Bola Ahmad Tinubu kan shugabancin kasar a watan Mayun shekara 2023 dai an yi hatsarin motocin daukar makamashi har sau a kalla 30, inda mutane kimani 500 suka rasa rayukansa sanadiyyar hakan.
A cikin yan makonni da suka gabata gwamnatin ta hana amfani da manyan-manyan motocin dakon mai masu daukar lita miliyon 60 saboda yawan hatsaron da suke yi.
Iran Press ta tattara bayanai da suka nuna cewa daga shekara 2009 zuwa watan maris na shekara ta 2025 an yi hatsurra tankuna daukar makamashi har 171 a kasar wanda ya lakume rayukan mutane 1,643. Na karshe kafin na jiya larabawa shi ne wanda ya kashe mutane 150 a jihar Jigawa a cikin watan Octoban shekarar da ta gabata.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Togo: An Yi Kiran Sake Yin Wata Sabuwar Zanga-zanagr Kin Jinin Gwamnati
Kungiyoyi farar da jam’iyyun adawar siyasa a kasar Togo, sun sake yin kira da a gudanar da Zanga-zanga a ranar 16 da 17 ga watan nan na Yuli da ake ciki.
Masu Zanga-zangar dai suna son nuna kin amincewa ne da siyasar hukumar kasar da suke bayyanawa da ta kama-karya, haka nan kuma kashe wasu mutane da aka yi a Zanga-zangar da ta gabata.
Bugu da kari, kiran a yi zanga-zangar dai ya zo ne bayan kama wasu ‘yan hamayyar siyasa da aka yi da kuam kara kudin wutar lantarki, da amince da sabon tsarin mulki da ya kara bai wa shugaban kasar Faure Gnassingbe karfin iko.
Wasu fitattun masu fafutuka a kasar, sun watsa sanarwa a shafukan sada zumunta da a cikin suke yin kiran mutane su fito domin yin Zanga-zangar ta wannan watan na Yuli.
Zanga-zangar karshe da aka yi a kasar, ta yi sanadiyyar mutuwar mutane 7 kamar yadda majiyar masu fafutukar ta ambata, sai dai kuma mahukuntan kasar sun ce, mutane biyu ne kadai su ka rasa rayukansu, kuma nustewa su ka yi a ruwa.
Har ila yau majiyar ‘yan hamayyar ta ce, an kame mutane da adadinsu ya kai 60 a yayin waccan Zanga-zangar.
A ranar 17 ga watan Yuli ne ake sa ran yin zaben kananan hukumomi, da jam’iyyun hamayya suke yin kira da a dage zaben zuwa wani lokaci a can gaba, har yanyin siyasar kasar ya bayar da dama.
A gefe daya, jam’iyyar da take Mulki a kasar ta dage taron da ta shirya yi a wannan Asabar din mai zuwa domin nuna goyon bayanta ga shugaban kasa, ba tare da bayyana dalilin yin hakan ba, kamar yadda kamfanin dillancin labarun Faransa ya nakato.