Mahara sun yi garkuwa da fiye da mutum 50 a Katsina
Published: 8th, April 2025 GMT
Mazauna yankin ƙaramar hukumar Funtua ta Jihar Katsina sun ce ’yan bindiga sun shiga wasu ƙauyukan yankin, inda suka kwashi mutane sama da 50 da suka hada da mata da ƙananan yara.
Maharan sun kuma kashe akalla mutum shida, inda suka sake kai wani hari a yankin Ƙaramar Hukumar Ɗandume ta jihar.
Rahotanni sun ce tun daga ranar Asabar maharan suka shiga yankin kuma ba su fita ba har zuwa ranar Lahadi da rana.
Malam Ya’u Ciɓauna mazaunin garin Layin Gara ne na Ƙaramar Hukumar Funtua, kuma ya ce “Misalin 10:30 na dare suka zo kuma sun kwashi maza da mata da ’yan mata da matan aure da kuma ƙananan yara har 53.
“Sun kashe mutum a Layin Gara na Ƙaramar Hukumar Funtua da kuma wasu mutum biyu a garin Mai Kwama a cikin Karamar Hukumar Ɗandume,” in ji Malam Ya’u.
Shi ma maigarin Layin Gara, Mustapha Abdullahi ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa mutanensa na cikin mawuyacin hali na rashin abinci, kwatsam kuma sai ga wannan matsala ta harin ’yan bindiga.
“Gwamnati tana ji tana gani wani abin ba a yi mana. Sojoji ma yadda ake turowa mu ba mu samu gatan an turo mana su ba, ’yan sandan da suka zo sai dai suka wuce suka nufi gardawa,” in ji Mustapha Abdullahi.
Matsalar tsaron dai ta tilasta wa mutanen yankin yin hijira da ɗan sauran abubuwan da suka rage masu, kamar yadda mai garin Layin Gara ke cewa.
Hukumar ’yan sanda a jihar ta Katsina dai ta ce tana kan bincike a kai lamarin, domin haka ba za ta ce komai ba sai ta kammala.
Matsalar tsaro na ci gaba da zama ƙarfen ƙafa a Jihar Katsina, kuma yayin da al’ummar da abin ya shafa ke ƙorafi da neman hukumomi su tashi tsaye wajen ba su kariya, gwamnati da sauran jami’an tsaro na cewa suna bakin ƙoƙarinsu wajen magance matsalar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗandume
এছাড়াও পড়ুন:
Iran ta damu da halin da ake ciki a yankin El Fasher na Sudan
Jamhuriyar Musulinci ta Iran, ta nuna damuwarta game da irin tashin hankali da ake ciki a Sudan musamman a yankin El Fasher.
Iran ta sake jaddada goyon bayanta ga ‘yancin Sudan, da hadin kai, da kuma cikakken yankin kasar yayin da tashin hankali ya mamaye kasar dake Arewacin Afirka.
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araghchi ne ya bayyana hakan yayin wata tattaunawa ta waray tarho da takwaransa na Sudan Mohiuddin Salem a ranar Juma’a.
Na farko ya nuna damuwa musamman game da hare-hare da kisan gillar da aka yi wa fararen hula a birnin El Fasher da ke kudu maso yammacin Sudan.
Duniya ta damu matuka a daidai lokacin da ake ci gaba da samun karuwar tashin hankali a Sudan.
A ranar Talata, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esmaeil Baghaei ya bayyana matukar damuwa game da rikice-rikicen makamai da ake ci gaba da yi a El Fasher, yana mai Allah wadai da lalata kayayyakin more rayuwa da kuma kisan fararen hula a birnin.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara November 1, 2025 Samia Suluhu Hassan ta lashe zaben shugaban kasa a Tanzaniya November 1, 2025 Najeriya ta musanta ikirarin Trump, na cewa Kristoci na fuskantar babbar barazana a kasar November 1, 2025 Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific November 1, 2025 Israila Ta Kai Hari Kan Ofishin kungiyar UNICEF Dake Gaza A November 1, 2025 Amurka Na Shirin Kai Hari Kan Kasar Venzuwela A Kowanne Lokaci November 1, 2025 Iran Ta Sanya Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3 October 31, 2025 Isra’ila Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza October 31, 2025 An Tube Yarima Mai Jiran Gado Na Birtaniya Bayan Da Aka Tabbatar Da Laifinsa October 31, 2025 Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta October 31, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci