MAGGI: Girke-girken Ramadan masu kawo sauyi da zumunta
Published: 21st, March 2025 GMT
Ramadan lokaci ne da ke hada kan iyalai da al’ummomi a fadin duniyar Musulmi. Lokaci ne da masoya ke haduwa tun daga lokacin sahur har zuwa buda-baki, ta hanyar kasancewa tare domin cin abinci mai gina jiki.
A wannan lokacin, ba a yin abinci don nishadi kawai, lokaci ne na inganta rayuwa da bayar da labarai na nishadantarwa da zumunta da kuma jin dadin kasancewa tare.
A cikin wannan labari mai ban sha’awa na MAGGI mai taken Labarin Ramadan, wasu mata biyar sun yi tafiya ta tsawon wata guda don samar da sauye-sauye, inda suka gano hadaddun girke-girke na sada zumunta da ke da alaka da samar da labarai masu jan hankali, har guda shida.
Tare da wasu jaruman wasan kwaikwayo da suka hada da Rekiya Attah, Labaran MAGGI na Ramadan suna kunshe da labarai masu kayatarwa, kuma masu dadi har na tsawon mako shida da aka fara tun farkon wannan watan na Ramadan. Wannan yanayi ya zame wa kowa jiki, to amma ya fi dadi a yayin da muka hadu a matsayinmu na iyali ko al’umma a lokacin Ramadan.
Kowane bangare na labarin yana nuna ainihin yadda lokacin Ramadana yake, ta fuskar son juna da zumunci da kuma yadda ake samun gamsuwa a lokacin buda-baki. Ta fuskar lokutan fahimtar juna da ba a yi tsammani ba ake yaukaka dangantaka da tabbatar da cewa, abokantaka tamkar tsintsiya ce madaurinink daya, inda take kawo kwanciyar hankali da annashuwa har ma a lokutan da ake cikin tsanani.
Da take magana a kan kudirin MAGGI na karfafa danganta da abokan huldasa a lokacin Ramadan tsawon shekara goma da suka gabata, Manajan Girki ta Kamfanin Nestlé Nigeria, Misis Rahamatou Palm-Zakari ta ce, “Ramadan lakaci ne na kyauta da soyayya, wanda MAGGI yake jaddadawa. Ta hanyar ci gaba da gabatar da samfuran da girke-girkenmu masu farin jini da samar da labaran Ramdan a yanzu, mun sadaukar da kanmu wajen ci gaba da yin kyakkyawan tasiri a rayuwar abokan huldarmu. Ta hanyar kayayyakin da muke samarwa da dandadon girki, za mu ci gaba da tallafa wa daidaikun mutane da iyalai wajen zabin abinci mai dandano da kara lafiya a kowace rana.
A matsayin kamfani da ya kudiri aniyar hada kan mutane ta hanyar abinci, MAGGI ya yi imani da muhimmancin burin samun abinci mai dandano.
MAGGI wani bangare ne na Kamfanin Nestlé, wanda kamfani da yake samar da abinci mai dandano da kyakkyawar rayuwa da ya kudiri aniyar bayyana irin rawar da abinci yake takawa wajen inganta rayuwa kowa da kowa a yanzu da kuma zamani mai zuwa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Maggi Tales of Ramadan Ramadan
এছাড়াও পড়ুন:
Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
Gwamnatin Tarayya ta roƙi ƙasashen Isra’ila da Iran da su daina rikici, su zauna lafiya su sasanta tsakaninsu.
A wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Waje ta fitar, ta bayyana damuwa kan yadda rikicin ke ƙara ta’azzara, inda ta nemi ɓangarorin biyu da su kai zuciya nesa don samar da zaman lafiya a duniya baki ɗaya.
Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — DalungSanarwar ta ce faɗa da ramuwar gayya na jefa rayukan fararen hula cikin hatsari, kuma yana iya haddasa rikici mai muni a yankin Gabas ta Tsakiya, wanda hakan zai iya barazana ga tsaron duniya da kuma ci gaban tattalin arziƙi dunuya.
“Mu a matsayimmu na ƙasa mai son zaman lafiya, muna roƙon ƙasashen da ke rikici da su zauna su tattauna maimakon su ci gaba da faɗa.”
Gwamnatin Tarayya ta kuma yi kira ga ƙasashen duniya, musamman Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya, da su ɗauki matakai don hana yaɗuwar rikicin da kuma samo hanyar warware matsalar.
Sanarwar ta ƙara da cewa amfani da ƙarfin soji ba shi da amfani matuƙa, domin faɗa ba zai kawo sauƙi ba.
Najeriya ta ce a shirye ta ke ta bayar da taimako domin hana yaɗuwar rikicin da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankin.