Aminiya:
2025-07-09@07:39:47 GMT

MAGGI: Girke-girken Ramadan masu kawo sauyi da zumunta

Published: 21st, March 2025 GMT

Ramadan lokaci ne da ke hada kan iyalai da al’ummomi a fadin duniyar Musulmi. Lokaci ne da masoya ke haduwa tun daga lokacin sahur har zuwa buda-baki, ta hanyar kasancewa tare domin cin abinci mai gina jiki.

A wannan lokacin, ba a yin abinci don nishadi kawai, lokaci ne na inganta rayuwa da bayar da labarai na nishadantarwa da zumunta da kuma jin dadin kasancewa tare.

A cikin wannan labari mai ban sha’awa na MAGGI mai taken Labarin Ramadan, wasu mata biyar sun yi tafiya ta tsawon wata guda don samar da sauye-sauye, inda suka gano hadaddun girke-girke na sada zumunta da ke da alaka da samar da labarai masu jan hankali, har guda shida.

Tare da wasu jaruman wasan kwaikwayo da suka hada da Rekiya Attah, Labaran MAGGI na Ramadan suna kunshe da labarai masu kayatarwa, kuma masu dadi har na tsawon mako shida da aka fara tun farkon wannan watan na Ramadan. Wannan yanayi ya zame wa kowa jiki, to amma ya fi dadi a yayin da muka hadu a matsayinmu na iyali ko al’umma a lokacin Ramadan.

Kowane bangare na labarin yana nuna ainihin yadda lokacin Ramadana yake, ta fuskar son juna da zumunci da kuma yadda ake samun gamsuwa a lokacin buda-baki. Ta fuskar lokutan fahimtar juna da ba a yi tsammani ba ake yaukaka dangantaka da tabbatar da cewa, abokantaka tamkar tsintsiya ce madaurinink daya, inda take kawo kwanciyar hankali da annashuwa har ma a lokutan da ake cikin tsanani.

Da take magana a kan kudirin MAGGI na karfafa danganta da abokan huldasa a lokacin Ramadan tsawon shekara goma da suka gabata, Manajan Girki ta Kamfanin Nestlé Nigeria, Misis Rahamatou Palm-Zakari ta ce, “Ramadan lakaci ne na kyauta da soyayya, wanda MAGGI yake jaddadawa. Ta hanyar ci gaba da gabatar da samfuran da girke-girkenmu masu farin jini da samar da labaran Ramdan a yanzu, mun sadaukar da kanmu wajen ci gaba da yin kyakkyawan tasiri a rayuwar abokan huldarmu. Ta hanyar kayayyakin da muke samarwa da dandadon girki, za mu ci gaba da tallafa wa daidaikun mutane da iyalai wajen zabin abinci mai dandano da kara lafiya a kowace rana.

A matsayin kamfani da ya kudiri aniyar hada kan mutane ta hanyar abinci, MAGGI ya yi imani da muhimmancin burin samun abinci mai dandano.

MAGGI wani bangare ne na Kamfanin Nestlé, wanda kamfani da yake samar da abinci mai dandano da kyakkyawar rayuwa da ya kudiri aniyar bayyana irin rawar da abinci yake takawa wajen inganta rayuwa kowa da kowa a yanzu da kuma zamani mai zuwa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Maggi Tales of Ramadan Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

Mutum 21 sun rasu a hatsarin mota a kan hanyar Zariya–Kano

Aƙalla mutum 21 ne suka rasu a wani mummunan hatsarin mota da ya auku a kan babban titin Zariya zuwa Kano.

Hukumar Kiyaye Haɗura ta Ƙasa (FRSC), reshen jihar ce ta tabbatar aukuwar hatsarin.

Hatsarin ya auku ne da misalin ƙarfe 8:23 na safe a unguwar Kasuwar Dogo da ke yankin Dakatsalle.

Zulum ya musanta shirin ficewa daga APC Gwamna ya gargaɗi sarakuna kan mamaye filayen kiwo a Gombe

Hatsarin ya rutsa da wata babbar mota ƙirar DAF mai lambar GWL 422 ZE da kuma motar ɗaukar fasinjoji ƙirar Toyota Hummer mai lambar KMC 171 YM.

FRSC, ta ce bincike ya nuna cewa direban motar fasinjojin ne ya karya doka ta hanyar bin hanyar da ba ta dace ba, wanda hakan ya sa suka yi karo da babbar motar.

Bayan aukuwar hatsarin, motocin biyu sun kama da wuta, inda mutane da dama suka ƙone ƙurmus.

Kwamandan FRSC na Kano, MB Bature, ya ce jami’ansu sun isa wajen cikin gaggawa bayan samun rahoto.

Sun kuma kira ma’aikatan kashe gobara na jihar da na tarayya domin kashe gobarar da kuma ceto waɗanda hatsarin ya rutsa da su.

Mai magana da yawun FRSC, Abdullahi Labaran, ya ce: “Mutum 24 ne hatsarin ya rutsa da su. Abin takaici, 21 sun rasu, yayin da uku suka jikkata.”

Gawarwakin da suka ƙone an kai su ɗakin ajiye gawa na Asibitin Nassarawa da ke Kano, yayin da waɗanda suka jikkata ke samun kulawa a Asibitin Gwamnati da ke Garun Malam.

Bayan haka, jami’an FRSC tare da taimakon ’yan sanda sun ɗauke motocin da suka tare hanya domin sauƙaƙa zirga-zirgar ababen hawa a titin.

Kwamanda Bature, ya bayyana alhininsa kan wannan mummunan lamari, tare da miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan waɗanda suka rasu.

Ya kuma yi wa waɗanda suka jikkata addu’ar samun sauƙi.

Ya kuma yi amfani da wannan dama wajen jan hankalin direbobi su guji karya doka; kamar bin hanya ba daidai ba da tuƙin ganganci, wanda hakan ke haddasa haɗura.

“Wannan lamari abin takaici ne wanda ke nuna muhimmancin bin ƙa’idojin hanya. Mafi yawan haɗura za a iya kauce musu idan direbobi za su kiyaye doka,” in ji Bature.

Ya kuma buƙaci direbobi, musamman na motocin haya, da su guji gudu fiye da ƙima da ganganci a hanya, wanda a cewarsa shi ne babban dalilin da ke haddasa haɗura da asarar rayuka.

Ga hotunan yadda hatsarin ya auku:

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • DAGA LARABA: Shin Ko Zafin Nema Na Kawo Samu?
  • Hukumar Abinci Ta Duniya ( WFP) Ta Jefa Wa Mutanane Kudancin Sudan Abinci Ta Sama
  • ‘Yan Gwagwarmayar Falasdinu Sun Halaka Sojojin Mamaya Biyar Tare Da Jikkata Wasu Goma Na Daban
  • Gwamnatin Tinubu na shirya mana zagon ƙasa — ADC
  • Mutane 21 Suka Mutu A Hatsarin Mota A Hanyar Zaria Zuwa Kano
  • An Kaddamar Da Shirin Samar Da Wutar Lantarki A Jami’ar Kashere Gombe.
  • Malamin Addinin Musulunci Yayi Kira Da Ayi Gaggawa Gyaran Hanyar Zamfara
  • Gwamna Yusuf Ya Kaddamar Rabon Na’urorin Rarraba Lantarki 500
  • Falasdinawa Kimani 635 Amurka da HKI Suka Kashe A Cibiyoyin Karban Abinci A Gaza
  • Mutum 21 sun rasu a hatsarin mota a kan hanyar Zariya–Kano