Leadership News Hausa:
2025-11-08@21:02:21 GMT

Azumi Ya Dara Wa Sauran Ibadu

Published: 21st, March 2025 GMT

Azumi Ya Dara Wa Sauran Ibadu

Shi wannan azumi, na wani lokaci ya fi na wani lokaci kamar an so a dinga yin azumi sau Uku a cikin kowanne wata, lokacin kwanan wata yana 13 da 14 da 15, wannan kwanaki hasken wata ya fi haske a cikinsu, to kamar yadda suke haske haka zuciyarka za ta kara haske sabida saduwa da hasken, sannan kuma hawa-hawa na musulunci guda Uku ne (Islam da Iman da Ihsan) to wanda ya riski wannan kwanaki Uku kamar Ya hau dukka wannan Matakan addinin ne.

Akwai azumin Litinin da Alhamis, azumin ranar Litinin Annabi (SAW) ne yake yi, an tambaye shi cewa Ya Rasulullahi sabida me kake azumin ranar Litinin? sai ya ce ranar ce aka haife ni, ina godiya ga Allah. To duk wanda ya yi azumin ranar Litinin ya yi koyi da Annabi (SAW) ne. Azumin ranar Alhamis kuma, Annabi (SAW) ya ce ranar ake nade ayyukan bayi na mako zuwa ga Ubangijinsu Rabbul Izzati, ina kwadayin a kai aikina ga Ubangiji ina azumi. Akwai sauran azumomin nafila da yawa.

Akwai babban azumin nafila da ake cewa ‘Na Annabi Dawudu’: Annabi Dawudu Mutum ne sarki mai ibada, yana daga cikin Ibadarsa azumi. In ya yi azumi yau, gobe sai ya ci abinci, haka ya kasance yanayi a rayuwarsa, idan ya rayu shekaru 60 – shekaru 30 ya yi azumi.

Allah yana gode wa Dan’adam in ya ce zai yi azumi duk ranar da yake so sai dai ba a so ya ware wata rana kamar Jumu’a ko Asabar ya dinga azumtarsu duk sati. Lallai azumi yana da falala sosai.

Allah ya wajabta mana azumi kamar yadda ya wajabta ma wadanda suka zo kafin mu.
An karba hadisi daga Mu’azu bin Jabal yana cewa: “Manzon Allah (SAW) bayan ya yi Hijira zuwa Madina, sai wata rana, Yahudawan Madina duka suka tashi da Azumi – Ashura, sai Annabi (SAW) Ya tambayesu lafiya, sai suka ba shi amsa da cewa ai wanna ranar ce Allah ya tseratar da Annabi Musa ya hallakar da Fir’auna, sai Annabi (SAW) yabce mu muka fi cancanta da Musa”. Annabi (SAW) ya yi umarnin cewa kowa ya ci gaba da azumin, shekara mai zuwa Allah ya saukar da azumin watan Ramadana, Annabi (SAW) ya ce Allah ya ba mu namu wanda ya so ya ci gaba da na Ashura, har Annabi (SAW) ya koma ga Allah yana azumin Ashura, azumin yana daga cikin manyan azumin Nafila a addinin Musulunci.

Ya zo cewa Annabi (SAW) ba ya barin azumin kwana Uku na kowanne wata. Idan mutum yana yin azumin kwana Uku na kowanne wata za a rubuta masa ladan kwana 30, sabida kowanne aiki daya ana rubuta masa goma, don haka azumin kwana uku dai-dai yake da uku sau Goma, Talatin kenan.

Allah ya wajabta azumin Watan Ramadana ga al’ummar musulmi bakidaya, amma a farko masu hali (dukiya) ciyarwa suke, marasa dama kuma su yi azumi, har sai da Allah yace “Wa’anta sumu khairullakum” sannan ya zama wajibi a kan kowa. Amma har gobe, yana nan marasa lafiya su kididdige kwanukan da suka tsere musu su biya a wasu ranaku bayan watan Ramadana, wadanda ba za su iya azumtar watan ba su ciyar, matafiyi in ba zai iya azumi cikin tafiyar ba, shi ma ya ciyar.

Yana daga cikin falalar watan Ramadana, Annabi (SAW) ya ce idan Watan Ramadana ya zo, duk kofofin Aljannah bude su ake yi, duk kofofin wuta kuma sai a kulle, kuma sai a kulle duk shaidanu, sai ka ga masallatai duk sun cika, sabida abokin yawon shaidancin an kulle shi. Ba ana nufin Aljannu da suke kama mutane ba na rashin lafiya, wannan ciwo ne, lada za a bai wa majinyacin, abokin yawon shaidancin ake daurewa.

Nasa’i ya ruwaito cewa kullum mai kira zai yi kira a cikin dare, yana cewa “ya kai mai neman alheri taho, ga watan alheri ya zo, ya kai mai neman sharri kame, wannan ba watan sharri ba ne.”

Wasu daga cikin Malamai sun tafi cewa ‘Ramadana’ sunan Allah ne sabida Hadisin Abi Hurairah da yake cewa “kar ku ce Ramadana ya zo, sabida Ramadana suna ne daga cikin sunayen Allah”. Allah a Littafinsa cewa ya yi “Shahru Ramadana…” Amma ba laifi in an ce Ramadana ya zo sabida ana nufin watan Ramadana.

Allah ya saukar da mafificin littafi (Alkur’ani) a cikin watan Ramadana, a mafificin dare (Lailatul Kadri).

An karba daga Abdullahi bin Abbas, Allah ya yarda da su, yake cewa “Allah Ya saukar da Alkur’ani daga lauhil mahfuzi izuwa saman Duniya (a cikin Ramadana aka saukar da alkur’ani daga lauhil mahfuzi zuwa saman Duniya, a dakin Baitul ilimi), Mala’ika Jibril (AS) shi kuma daga nan yake debo ayoyinsa zuwa ga Annabi (SAW), sai da ya shafe shekaru 23 yana kan wannan aikin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: watan Ramadana azumin ranar

এছাড়াও পড়ুন:

Karuwar Matsalar Jin Kai Mafi Girma A Duniya A Sudan Saboda Ci Gaba Da Masifar Yaki A Kasar

Sudan na fuskantar matsalar jin kai mafi girma a duniya a daidai lokacin da ake kara samun karuwar fada a Darfur da El Fasher

Asusun Kula da kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) ya yi gargadin cewa: Matsalar karancin abinci mai gina jiki ta kara ta’azzara a Sudan, yana mai tabbatar da cewa matsalar karancin abinci mai gina jiki ta wuce matakin gaggawa a cikin sama da kashi 60 cikin 100 na yankunan. A halin yanzu, shugaban Majalisar Gudanar da Mulki a Sudan, Abdel Fattah al-Burhan, ya jaddada kudurin rundunar sojin kasar na tabbatar da tsaron dukkan iyakokin Sudan da kuma murkushe ‘yan tawayen.

Wani sabon gargadin Majalisar Dinkin Duniya ya sanya Sudan a kan gaba wajen fuskantar bala’in jin kai da ba a taba ganin irinsa ba. UNICEF ta bayyana cewa matsalar karancin abinci mai gina jiki ta wuce matakin gaggawa a cikin sama da kashi 60 cikin 100 na yankunan da aka yi bincike a kansu, a yayin da fada ke kara kamari da kuma kwararar ‘yan gudun hijira a Darfur.

A cikin rahotonta, UNICEF ta kara da cewa ta gudanar da bincike a wurare 88 tsakanin watan Janairu da Yuli na wannan shekarar, inda ta bayyana cewa kashi 80 cikin 100 na Darfur, musamman a arewacin yankin, sun sami karuwar rashin abinci mai gina jiki ta wuce matakin gaggawa na kashi 15 cikin 100.

Rahoton ya tabbatar da cewa adadin yaran da ke fama da rashin abinci mai gina jiki ya karu zuwa sama da 315,000 a rabin farko na shekarar, karuwar kusan kashi 48 cikin 100 idan aka kwatanta da wannan lokacin a bara. Yayin da matsalar abinci ke ƙara ta’azzara, haka nan wahalar waɗanda suka ƙaura daga El Fasher zuwa Tawila a Arewacin Darfur ke ƙaruwa.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka An Rantsar Da Paul Biya A Matsayin Shugaban Kamaru Karo Na Takwas November 7, 2025 Dakarun Sojin Kasar Sudan Sun yi Watsi Da Batun Dakatar Da Bude Wuta Da Amurka Ta Gabatar November 7, 2025 Zanga zanga Ta Barke A Birmingham Ta Nuna Kin Jinin Isra’ila . November 7, 2025 Pezeshkiyan: Masu Kawo Rarraba Tsakanin Musulmi Suna yi wa Yan Sahayuniya Aiki Ne November 7, 2025 Shugaban Najeriya Bola Tinubu Ya yi Alwashin Kawo Karshen Ta’addanci A Kasar November 7, 2025 Araqchi Ya Ce: Harin Amurka Kan Kasar Venezuela Ya Bayyana Karara Duniya Tana Gani November 6, 2025 Qalibaf: Iran Da Pakistan Zasu Aiwatar Dukkan Yarjejeniyar Da Suka Cimma A Tsakaninsu November 6, 2025 Kwamitin Tsaro Ya Ce: Amurka Ta Bukaci Duba Kudurin Neman Kafa Rundunar Kasa Da Kasa A Gaza November 6, 2025 Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kashe Mutum Guda Tare Da Jikkata Wasu Uku A Kudancin Lebanon   November 6, 2025 Sayyid Muqtada al-Sadr Ya Fadakar Da Magoya Bayansa Kwanaki Kafin Zabe A Iraki November 6, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala
  • Karramawar LEADERSHIP Gare Ni, Zaburantarwa Ce Ga Ci Gaba Da Kyawawan Manufofin Mu – Gwamna Lawal
  • Ɗan shekara 2 ya rasu bayan faɗawa rijiya a Kano
  • Ma’aikacin jinya ya kashe marasa lafiya 10 saboda aiki ya masa yawa
  • Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)
  • Karuwar Matsalar Jin Kai Mafi Girma A Duniya A Sudan Saboda Ci Gaba Da Masifar Yaki A Kasar
  • Kamfanin wutar lantarki na Abuja ya salami ma’aikata 800
  • An rantsar da shugaban Kamaru Paul Biya karo na 8
  • Najeriya ta yi watsi da sanya sunanta cikin jerin kasashen da ake tauye ’yancin addini
  • Za a gudanar da wasannin ƙwallon yashi a Abuja