Sharhin Bayan Labarai: Zanga-Zanga A Kasashen Larabawa Ta Goyon Bayan Falasdinaw A Gaza
Published: 7th, April 2025 GMT
Assalamu alaikujml/m masu sauraro, sharhin bayan labarummu zai yi magana danagne da zanga-zanga masu yawa wadanda ake yi a kasashen larabawa a dai dai lokacinda HKI take kara tsananta kisan kiyashi a yankin Zirin gaza, wanda ni tahir amin zan karanta.
////.. Madalla, a dai-dai lokacin da sojojin HKI suke kara yawan hare-haren da suke kaiwa Falasdinawa a Gaza, da kuma yadda suke kara kissan kiyashi a yankin, an gudanar da zanga-zanga a kasashen larabawa da dama a ranar litinin, inda mutane a birnin Damaskus na kasar Siriya suka fito kan tituna a birane da dama a kasar suke allawadai da HKI da kuma karin dauke rayukan falasdinawa da take yi a Gaza.
Kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran ya nakalto masu zanga zanga a birnin Damaskus suna allawadai da HKI, kan hare-hare da kuma kisan kiyashin da take yi a gaza da kuma hare haren da suke kaiwa a cikin kasar ta Siriya na lalata cibiyoyin tsaron kasar da kuma wadanda take kaiwa kan lardin Dra’a dake kudancin kasar sannan sun roki All..rahama ga wadanda suka yi shahada a lardin.
A birnin Halab kuma daliban Jami’ar birnin ne suka fito zanga-zanga suna allawadai da HKI da kuma kissan da take yi a Gaza, sun kuma rera shi’ar, mai cewa (gaba dayammu shahidai ne). Muna kuma goyon bayan gwagwarmayan Falasdinawa a Gaza da sauran yankuna a yankin yamma da kogin Jordan.
A birnin Hama kuma daliban jami’ar birnin ne suka fito zanga-zanga suna allawadai da HKI, da kuma goyon baya ga gwagwarmayan da Falasdinawa suke yi da HKI.
Sai kuma kasar Morocco inda daliban kanan makarantu da kuma daliban jami’o’iin kasar suka fito gangami a cikin birane da garuruwan kasar inda suke allawadai da kisan kiyashin da sojojin HKI take yi a Gaza, suna kuma goyon bayan Falasdinawa a gwagwarmayan da suke yi don samun yencin kasarsu wacce aka mamaye.
Sai kuma kasar Jordan inda daliban Jami’a a birnin Amman suka gudanar da gangami a cikin Jami’ar Amman babban birnin kasar suke kuma allawadai da kissan kiyashin da sojojin HKI suke yi a Gaza, sannan sun nuna goyon bayansu ga al-ummar Falasdinu. Kafafen yada labarai a kasar Jordan sun bada labarin cewa daliban jami’ar Amman sun yi tir da kissan Falasdinawa a Gaza, suna kuma kira ga kasashen larabawa , da kasashen musulmi da kuma duk wani mai yenci a duniya ya tashi ya taimaka don kubutar da Falasdinawa daga halin da suke ciki.
Sai kuma birnin Ramallah na kasar Falasdinu da aka mamaye, masu zanga –zanga suka rera taken girmama shahid Muhammad Dhaif babban kwamnadan dakarun izzuddeen Qassam wanda sojojin yahudawan suka kai ga shahada a cikin yan watannin da suka gabata.
Sannan a areawacin kasar Lebanon kuma, mutanen birnin Tarabulos sun fiti zanga-zangar yan allawadai da yahudawan da kuma kissan kiyashin da suke yi a gaza.
A birnin Tunis na kasar Tunisiya daliban jami’o’ii a kasar sun fito kan tituna a birnin suna allawadai da HKI da kima laifukan yakin da suke aikatawa a kasar Falasdinu. Labaran sun bayyana cewa a garin Susah da kuma Safaqs na kasar mutanen da dama sun fito kan tityuna inda suke allawadai da yahudawan sahyoniya.
Masana da dama suna ganin mafi yawan mutanen kasar Larabawa basa kaunar yahudawan sahyoniyya, amma wasu daga cikin shuwagabanninsu ne suke tare da yahudawan, harma wasu daga cikinsu na kokarin samar da huldar jakadanci da su.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: suna allawadai da HKI Falasdinawa a kiyashin da
এছাড়াও পড়ুন:
Kasar Iran Ta Musanta Yin Katsalandan A Tattaunawar Neman Tsagaita Bude Wuta A Gaza
Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta musanta zargin yin katsalandan a tattaunawar tsagaita bude wuta a Gaza
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran, Ismail Baqa’i, ya musanta zargin katsalandan din Iran a tattaunawar tsagaita bude wuta a Gaza.
A yayin da yake amsa tambaya game da ikirarin da shugaban kasar Amurka ya yi na cewa Iran na tsoma baki a shawarwarin tsagaita bude wuta a zirin Gaza, ya ce: Jamhuriyar Musulunci ta Iran tare da dukkan kasashen duniya tana yin kakkausar suka kan kisan gillar da ake yi a Gaza tare da goyon bayan duk wani tsari da zai kai ga dakatar da aikata laifuka da kuma rage radadin wahalhalun da al’ummar Gaza suke ciki.
Baqa’i ya jaddada cewa; Masu yin shawarwarin Hamas sun fahimci bukatar neman cimma muradun al’ummar Gaza da ake zalunta ta hanyar da ta dace, kuma ba sa bukatar shiga tsakani na bangarori na uku dangane da hakan.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Iran ya yi la’akari da katsalandan din Iran a cikin shawarwarin da suka dace da cewa ba shi da tushe balle makama, yana mai jaddada cewa irin wadannan zarge-zarge wani nau’i ne na neman tauyaye hakki da gujewa hakkin da ya rataya a wuyar mutum da kokarin Amurka na gujewa duk wani mugun aiki da gwamnatin ‘yan sahayoniyya ta aikita kan al’ummar Falasdinu, da suka hada da kisan fararen hula 60,000 da ba su ji ba ba su gani ba, da suka hada da mata da kananan yara da kuma killace Zirin Gaza tsawon watanni. Da hana shigar agajin jin kai da kuma kashe fararen hula da ke fama da yunwa da kishirwa a tarkon kisa a wuraren da ake kira cibiyoyin rarraba kayan agaji da wata cibiyar Amurka ta kafa.