Sharhin Bayan Labarai: Zanga-Zanga A Kasashen Larabawa Ta Goyon Bayan Falasdinaw A Gaza
Published: 7th, April 2025 GMT
Assalamu alaikujml/m masu sauraro, sharhin bayan labarummu zai yi magana danagne da zanga-zanga masu yawa wadanda ake yi a kasashen larabawa a dai dai lokacinda HKI take kara tsananta kisan kiyashi a yankin Zirin gaza, wanda ni tahir amin zan karanta.
////.. Madalla, a dai-dai lokacin da sojojin HKI suke kara yawan hare-haren da suke kaiwa Falasdinawa a Gaza, da kuma yadda suke kara kissan kiyashi a yankin, an gudanar da zanga-zanga a kasashen larabawa da dama a ranar litinin, inda mutane a birnin Damaskus na kasar Siriya suka fito kan tituna a birane da dama a kasar suke allawadai da HKI da kuma karin dauke rayukan falasdinawa da take yi a Gaza.
Kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran ya nakalto masu zanga zanga a birnin Damaskus suna allawadai da HKI, kan hare-hare da kuma kisan kiyashin da take yi a gaza da kuma hare haren da suke kaiwa a cikin kasar ta Siriya na lalata cibiyoyin tsaron kasar da kuma wadanda take kaiwa kan lardin Dra’a dake kudancin kasar sannan sun roki All..rahama ga wadanda suka yi shahada a lardin.
A birnin Halab kuma daliban Jami’ar birnin ne suka fito zanga-zanga suna allawadai da HKI da kuma kissan da take yi a Gaza, sun kuma rera shi’ar, mai cewa (gaba dayammu shahidai ne). Muna kuma goyon bayan gwagwarmayan Falasdinawa a Gaza da sauran yankuna a yankin yamma da kogin Jordan.
A birnin Hama kuma daliban jami’ar birnin ne suka fito zanga-zanga suna allawadai da HKI, da kuma goyon baya ga gwagwarmayan da Falasdinawa suke yi da HKI.
Sai kuma kasar Morocco inda daliban kanan makarantu da kuma daliban jami’o’iin kasar suka fito gangami a cikin birane da garuruwan kasar inda suke allawadai da kisan kiyashin da sojojin HKI take yi a Gaza, suna kuma goyon bayan Falasdinawa a gwagwarmayan da suke yi don samun yencin kasarsu wacce aka mamaye.
Sai kuma kasar Jordan inda daliban Jami’a a birnin Amman suka gudanar da gangami a cikin Jami’ar Amman babban birnin kasar suke kuma allawadai da kissan kiyashin da sojojin HKI suke yi a Gaza, sannan sun nuna goyon bayansu ga al-ummar Falasdinu. Kafafen yada labarai a kasar Jordan sun bada labarin cewa daliban jami’ar Amman sun yi tir da kissan Falasdinawa a Gaza, suna kuma kira ga kasashen larabawa , da kasashen musulmi da kuma duk wani mai yenci a duniya ya tashi ya taimaka don kubutar da Falasdinawa daga halin da suke ciki.
Sai kuma birnin Ramallah na kasar Falasdinu da aka mamaye, masu zanga –zanga suka rera taken girmama shahid Muhammad Dhaif babban kwamnadan dakarun izzuddeen Qassam wanda sojojin yahudawan suka kai ga shahada a cikin yan watannin da suka gabata.
Sannan a areawacin kasar Lebanon kuma, mutanen birnin Tarabulos sun fiti zanga-zangar yan allawadai da yahudawan da kuma kissan kiyashin da suke yi a gaza.
A birnin Tunis na kasar Tunisiya daliban jami’o’ii a kasar sun fito kan tituna a birnin suna allawadai da HKI da kima laifukan yakin da suke aikatawa a kasar Falasdinu. Labaran sun bayyana cewa a garin Susah da kuma Safaqs na kasar mutanen da dama sun fito kan tityuna inda suke allawadai da yahudawan sahyoniya.
Masana da dama suna ganin mafi yawan mutanen kasar Larabawa basa kaunar yahudawan sahyoniyya, amma wasu daga cikin shuwagabanninsu ne suke tare da yahudawan, harma wasu daga cikinsu na kokarin samar da huldar jakadanci da su.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: suna allawadai da HKI Falasdinawa a kiyashin da
এছাড়াও পড়ুন:
Isra’ila ta hana ayarin motocin agaji na arewacin Afrika shiga Gaza
Ministan yakin Isra’ila, Israel Katz, ya umarci sojojin kasar da su hana ayarin motocin agaji na arewacin Afirka shiga yankin Zirin Gaza da aka yi wa kawanya.
A cikin wata sanarwa ofishin Katz ya umarci sojojin Isra’ila da su hana “masu fafatuka daga Masar shiga yankin Zirin Gaza.
Katz bukaci “Hukumomin Masar dasu hana zuwan masu fafatukar a kan iyakar Masar da Isra’ila.”
Ministan ya ya bayyana hakan a matsayin hadari ga jami’an tsaron Isra’ila na IDF.”
Wannan dai na zuwa ne bayan ayarin motoci 100 da ya kunshi dubban masu fafatuka daga kasashen Morocco, Aljeriya, Tunisia, Libya da Masar, suka yunkuri anniyar wayar da kan al’ummar duniya kan matsalar jin kai a Gaza, da neman kawo karshen yakin kisan kare dangi, da karya shingen da Isra’ila ke yi da kuma kai muhimman kayayyakin jin kai a Gaza.
Ayarin da ya kunshi kungiyoyin kwadago da masu fafutukar kare hakkin bil’adama da ‘yan wasa da lauyoyi da likitoci da ‘yan jarida da na kungiyoyin matasa da dai sauransu ana sa ran za su shiga Masar a yau Alhamis kafin isa mashigar Rafah da ke kan iyaka a kudancin zirin Gaza.
Kafin hakan dama sojojin Isra’ila sun kwace jirgin ruwan agaji na Madleen da ke kan hanyarsa ta zuwa Gaza domin kai tallafi ga al’ummar Zirin, bayan shafe sama da watanni ashirin na yakin kisan kare dangi da Isra’ila ke yi.
An kama dukkan masu fafutukar na kasa da kasa su 12 da ke cikin jirgin, ciki har da mai fafutukar Sweden Greta Thunberg.