Iran ta yi Allah wadai da Kwamitin Sulhun na MDD na rashin tabaka komai wajen  dakatar da ayyukan Amurka da Isra’ila wanda Iran din ta bayyana da abin kunya.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya yi tir da munanan hare-haren da jiragen yakin Amurka suka kai kan kasar Yemen da kuma yadda gwamnatin Isra’ila ke ci gaba da kai wa Falasdinawa hari a zirin Gaza, tare da yin Allah wadai da rashin daukar wami mataki daga kwamitin sulhu na fuskantar wadannan munanan ayyukan.

Esmaeil Baghaei, a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis, ya bayyana matukar na dama kan yadda ake kashe fararen hula da suka hada da mata da kananan yara da ba su ji ba ba su gani ba, da kuma lalata muhimman ababen more rayuwa na kasar Yemen, sakamakon hare-haren da Amurka ke kaiwa.

Ya bayyana hare-haren da Amurka ta kai ta sama a matsayin laifukan yaki da laifukan ta’addanci, yana mai danganta hakan da “abin kunya da rashin gaskiya” na kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da sauran cibiyoyin kasa da kasa kan wannan ta’asa.

Ya ce Amurka da gwamnatin yahudawan sahyoniya sun kitsa wani shiri na hadin gwiwa na raunana al’ummar musulmi da kuma rufe duk wata muryar goyon baya ga al’ummar Falastinu da ake zalunta.

Daga karshe Baghaei ya jaddada nauyin da ya rataya a wuyan kasashen musulmi na duniya na dakatar da zaluncin da Isra’ila ke yi da kuma hare-haren da sojojin Amurka suke yi a kan Falasdinawa da sauran al’ummar musulmi, yana mai kira ga gwamnatocin musulmi da su dauki matakin da ya dace da kuma kokarin da kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC ke yi na shawo kan lamarin.

Akalla Falasdinawa 436 da suka hada da kananan yara 183 ne aka kashe tun bayan da Isra’ila ta keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza a ranar Talata.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: hare haren da da Isra ila

এছাড়াও পড়ুন:

Talata ce ɗaya ga watan Zhul Qi’ida — Sarkin Musulmi

Sarkin Musulmi, Alhaji Abubakar Muhammad Sa’ad, ya bayyana cewa gobe Talata, 30 ga watan Afrilun 2025, ita ce za ta kasance 1 ga watan Zhul Qi’ida na shekarar 1446 ta Hijiriyya.

Wata sanarwa da shugaban kwamatin ganin wata na fadar, Farfesa Sambo Wali ya fitar ta ce an ɗauki matakin ne saboda ba a ga jinjirin watan ba a ranar Lahadi.

Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku Rasha ta ayyana tsagaita wuta ita kaɗai a yakinta da Ukraine

Hakan na nufin yau Litinin, 28 ga watan Afrilu ne 30 ga watan Ƙaramar Sallah na Shawwal.

A ƙa’idar kalandar Musulunci, kowane wata yana yin kwana 29 ne, amma idan ba a ga jaririn watan ba sai a cika shi zuwa kwana 30.

Aminiya ta ruwaito cewa tun a ranar Asabar da ta gabata ce Fadar Sarkin Musulmin ta ba da umarnin duban watan na Zhul Qi’ida.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tarayyar Afirka ta dage takunkumin da ta kakabawa Gabon
  • Amurka ta sake laftawa wasu kamfaninin mai na Iran takunkumi
  • Katafaren Jirgin Daukar Jiragen Yaki Na Kasar Amurka Harry Truman Zai Fice Daga Tekun Maliya
  • Nazarin CGTN: Ana Kara Bayyana Rashin Gamsuwa Da Sabuwar Gwamnatin Amurka Daga Ciki Da Wajen Kasar
  • Rashin tsaro: Gwamnan AbdulRahman Ya Gana Da Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Jihar Kwara 
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Quneitra Na Kasar Siriya Tare Da Kafa Shingen Bincike
  • Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana
  • Talata ce ɗaya ga watan Zhul Qi’ida — Sarkin Musulmi
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Tattauana Da Shugaban Hukumar IAEA
  • Takht Ravanji: Iran Ba Za Ta Taba Yin Tattaunawa Akan Dakatar Da Tace Sanadarin Uranium Ba