Iran ta yi Allah wadai da Kwamitin Sulhun na MDD na rashin tabaka komai wajen  dakatar da ayyukan Amurka da Isra’ila wanda Iran din ta bayyana da abin kunya.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya yi tir da munanan hare-haren da jiragen yakin Amurka suka kai kan kasar Yemen da kuma yadda gwamnatin Isra’ila ke ci gaba da kai wa Falasdinawa hari a zirin Gaza, tare da yin Allah wadai da rashin daukar wami mataki daga kwamitin sulhu na fuskantar wadannan munanan ayyukan.

Esmaeil Baghaei, a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis, ya bayyana matukar na dama kan yadda ake kashe fararen hula da suka hada da mata da kananan yara da ba su ji ba ba su gani ba, da kuma lalata muhimman ababen more rayuwa na kasar Yemen, sakamakon hare-haren da Amurka ke kaiwa.

Ya bayyana hare-haren da Amurka ta kai ta sama a matsayin laifukan yaki da laifukan ta’addanci, yana mai danganta hakan da “abin kunya da rashin gaskiya” na kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da sauran cibiyoyin kasa da kasa kan wannan ta’asa.

Ya ce Amurka da gwamnatin yahudawan sahyoniya sun kitsa wani shiri na hadin gwiwa na raunana al’ummar musulmi da kuma rufe duk wata muryar goyon baya ga al’ummar Falastinu da ake zalunta.

Daga karshe Baghaei ya jaddada nauyin da ya rataya a wuyan kasashen musulmi na duniya na dakatar da zaluncin da Isra’ila ke yi da kuma hare-haren da sojojin Amurka suke yi a kan Falasdinawa da sauran al’ummar musulmi, yana mai kira ga gwamnatocin musulmi da su dauki matakin da ya dace da kuma kokarin da kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC ke yi na shawo kan lamarin.

Akalla Falasdinawa 436 da suka hada da kananan yara 183 ne aka kashe tun bayan da Isra’ila ta keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza a ranar Talata.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: hare haren da da Isra ila

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Kaddamar Da Hare-hare Kan Iran

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Ce Ba’a Rufe Kofar Diblomasiyya Ba, Matukar HKI Ta Dakatar Da Kaiwa Kasar HKI
  • Iran Ta Sanar Da Dakatar Da Tattaunawa Da Amurka A Wannan Lokaci Da Take Fuskantar Yaki Daga Isra’ila
  • Kungiyar Abokan Yarjejeniyar M.D.D Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ke Kai Wa Kan Iran
  • Iran ta sake kai hare-haren martani kan Isra’ila
  • Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba
  • Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Kaddamar Da Hare-hare Kan Iran
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Bude Kofofin Jahannama Ga Yahudawan Sahayoniyya
  • Iran, ta yi wa Isra’ila ruwan makamai masu linzami
  • Iran : harin da Isra’ila ta kai ‘ ayyana yaki’ ne_ Araghchi
  • NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya