Leadership News Hausa:
2025-09-18@05:40:52 GMT

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [13]

Published: 21st, March 2025 GMT

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [13]

Ibnu Juzai al-Kalbi Allah Ya yi masa ranama yan nuna mana munin hassada ta fuska biyu:

1. A Ɗabi’a: Hassada tana haifar da cutar zuciya, wadda ke hana mutum farin ciki da jin daɗin rayuwa, kuma tana sa mai yin ta ya zama mai mugun hali, da ƙoƙarin ganin wani ya faɗi ko ya rasa abin da ya samu. A al’ada, mutane suna ƙin mai hassada saboda halayensa na rashin son alheri ga mutane da kuma fatan sharri a gare su.

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [12] Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [11]

2. A Shari’a: A cikin Alƙur’ani, Allah ya yi umurni da a nemi tsari a wurinsa daga hassadar mahassadi, inda Ya ce:” Ka ce:” Ina neman tsari da Ubangijin asuba. Daga sharrin abin da Ya halitta. Da kuma sharrin dare idan ya lulluɓe da duhu. Da kuma sharrin mata masu tofi a cikin ƙulle-ƙulle. Da kumma sharrin mahassadi yayin da ya yi hassada.” Suratul Falaƙ aya ta 1-5. Manzon Allah (ﷺ) ya ce: “Kada ku yi hassada da juna…” Muslim ne ya ruwaito [#2563].

Hassada tana iya kai mutum ga saɓawa Allah, kamar yadda Shaiɗan ya ƙi yin sujada ga Adam saboda kishi da hassada. Hassada tana haifar da cin amanar ‘yan’uwa, da munafunci, da karya. Hassada tana cutar da mai yin ta fiye da wanda ake yi wa. A ɗabi’a, tana hana kwanciyar hankali, a shari’a kuwa tana kai mutum ga zunubi. Maimakon yin hassada, Musulumi ya kamata ya roƙi Allah ya ba shi alheri kamar yadda Ya ba wa waninsa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Abu Razina Nuhu Ubale Paki Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno

Sojojin Najeriya sun kashe aƙalla mayakan ƙungiyar ISWAP 8, ciki har da manyan kwamandojinta biyu a Jihar Borno.

Wata majiyar leƙen asiri daga rundunar haɗin kai ta OPHK ta bayyana cewa an kashe ’yan ta’addan ne a wata arangama da suka yi da sojojin a kan hanyar Maiduguri zuwa Baga a safiyar ranar Litinin.

DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala

A cewar majiyoyin, an yi arangamar ce a kusa da Garin Giwa da ke gab da ƙauyen Kauwa, lokacin da ’yan ta’addan suka yi wa dakarun da ke sintiri kwanton ɓauna.

“A yayin wannan artabu, an kashe ’yan ta’adda takwas, ciki har da Munzirs biyu (kwamandojin filin daga na ƙungiyar) da kuma Qaid ɗaya (shugaban sashe).

“An kashe Modu Dogo, Munzir daga Dogon Chukun, wani Munzir da ba a bayyana ba, da Abu Aisha, shugaban sashe (Qaid) daga Tumbun Mota,” in ji wata majiya.

Majiyar ta ƙara da cewa wasu mayaƙa da dama sun samu raunuka, musamman waɗanda suka tsere da ƙafa bayan sun yi watsi da babura 14 da sojojin suka ƙwato.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karamar Hukumar Malam Madori Ta Horar Da Mata Kare Kai Daga Cututtukan Mahaifa
  • Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
  •  Gaza: HKI Tana Ci Gaba Da Yi Wa Falasdinawa  Kisan Kiyashi A Gaza
  • NECO ta saki sakamakon jarabawar 2025
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Baqa’i: Kowace Kasa A Duniya Tana Da Hakkin Mallakar Makamashin Nukiliya Na Zaman Lafiya
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar