Aminiya:
2025-09-18@00:48:40 GMT

Hatsarin mota ya kashe mutane 5 a Yobe

Published: 8th, April 2025 GMT

Aƙalla mutane biya ne suka mutu, 19 suka yi munanan raunuka a dalilin hatsarin mota da ya rutsa da su a Kasuwar Damagum da ke kan babbar hanyar Kano-Maidugri a Jihar Yobe.

Lamarin ya auku ne da misalin ƙarfe 1:00 na ranar Lahadi.

Saudiyya ta sanya wa masu Umarah wa’adin ficewa daga ƙasar Gobara ta laƙume ƙauyuka a Borno

Wani da lamarin ya faru a idonsa, ya shaida wa Aminiya cewa, gudun wuce sa’a da wani direban bas ke yi ne ya janyo hatsarin, inda ya afka wa mutanen da ke tsaye a bakin titi ana tsaka da cin kasuwar.

“Direban ya ɗauko fasinjoji ne zuwa Damaturu, kuma da alamu Potiskum ya  nufa,” in ji shi.

Kwamandan hukumar kiyaye haɗura ta ƙasa reshen Jihar Yobe, CC Livinus Longzen Yilzoom, ya tabbatar da mutuwar mutane biyar, yayin da 19 kuma suka samu raunuka.

Daga nan ne kuma ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan waɗanda suka rasu, da kuma al’ummar Damagum da Jihar Yobe baki ɗaya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hatsarin mota

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

Ya ce ya sayi layin wayar ne daga hannun wani Audu, ɗan kungiyar Vikings wanda ya tsere yanzu.

A wani lamari kuma, ‘yansanda sun kama wasu mutum huɗu da suka shiga gonar wani mutum a Lapai Gwari, inda suka saci kifi da darajar kuɗinsu ta kai Naira 750,000.

Babban wanda ake zargi, Hussaini Garba, ya amsa laifi tare da bayyana Ahmed Yusuf, Ibrahim Musa da Abdulazeez Bawa a matsayin mutanen da suke sayen kifin idan ya sato.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Kungiyar Kare Hakkokin Bil’Adama Ta Siriya Ta Bankado Karin Fararen Hula Da Aka Kashe A Rikicin Suweida
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara