Aminiya:
2025-06-15@07:34:33 GMT

Wike ya ƙwace filin Sakatariyar PDP da ke Abuja

Published: 18th, March 2025 GMT

Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya ƙwace wani fili mallakar sakatariyar Jam’iyyar PDP da ke Abuja.

Hakan na ƙunshe ne cikin wata wasiƙa mai ɗauke da sa hannun shugaban sashen kula da filaye na Abuja, Chijioke Nwankwoeze.

Nwankwoeze ya ce an yanke hukuncin ƙwace filin ne sakamakon gazawar babbar jam’iyyar adawar na biyan kudin gini na shekara shekara.

Wasiƙar ta ce PDP ta gaza biyan kuɗin tun daga ranar 1 ga watan Janairun 2006 zuwa 1 ga watan Janairun 2025, duk da sanarwar da hukumar gudanarwar babban birni (FCTA) ta wallafa a jaridu da dama tun daga shekarar 2023 kan buƙatar biyan kuɗaɗen.

Aminiya ta ruwaito cewa filin na Jamiyyar PDP na daga cikin filaye 4,700 da Ministan ya ƙwace a Abuja.

 

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Mutum ɗaya ya tsira da ransa cikin 242 a hatsarin jirgin India

Jirgin saman fasinja da ke kan hanyarsa ta zuwa Landan wanda ya yi hatsari a birnin Ahmedabad na Indiya a ranar Alhamis.

Mutum ɗaya ne ya tsira daga cikin mutane 242 da ke cikin jirgin, tare da fasa gine-ginen likitoci da iyalansu.

Wani ɗan jarida na AFP ya ga gawarwakin da aka zaƙulo daga wurin da jirgin ya faɗi, da kuma bayan jirgin ƙirar Boeing 787-8 Dreamliner a rataye a gefen wani gini da ya rutsa da shi a lokacin cin abinci.

Mayar da Nijeriya tsarin jam’iyya ɗaya ba ya cikin manufofinmu — Tinubu An ciro gawarwaki sama da 200 daga jirgin Indiya da ya yi hatsari

“Iftila’in da ya afku a Ahmedabad ya ba mu mamaki da kuma ɓacin rai. Abin takaici ne da ba za a iya cewa komai ba,” in ji Firayim Minista Narendra Modi a bayaninsa bayan jirgin Air India mai lamba 171 ya yi hatsari bayan tashinsa.

Kwamishinan ’yan sandan birnin GS Malik ya ce gawarwakin fasinjoji da waɗanda abin ya rutsa da su a ƙasa na daga cikin 204 da aka gano zuwa yanzu, yayin da ma’aikatan lafiya ke jinya da dama waɗanda suka jikkata a birnin.

Yayin da aka fara fargabar mutuwar duk wanda ke cikin jirgin, jami’in kula da lafiya na jihar Dhananjay Dwivedi ya shaida wa AFP cewa “an tabbatar da wanda ya tsira” kuma ana jinyar shi a asibiti.

Ɗan jaridar na AFP ya ga wani gini ya ƙone ƙurmus bayan faɗuwar jirgin, inda hayaƙi ya turnuke sama da wani ɓangare na jirgin a ƙasa.

“Rabin jirgin ya faɗo cikin ginin mazaunin da likitoci ke zaune tare da iyalansu,” in ji Krishna, wani likita da bai bayyana cikakken sunansa ba.

Krishna ya ce ya ga “kusan gawarwaki 15 zuwa 20 da suka ƙone”, yayin da shi da abokan aikinsa suka ceto ɗalibai kusan 15.

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Indiya ta ce, akwai mutane 242 a cikin jirgin, ciki har da matuƙan jirgi biyu da ma’aikatan cikin jirgin 10.

Kamfanin jirgin Air India ya ce, akwai fasinjojin Indiya 169 da 53 ‘yan Burtaniya da ‘yan Portugal bakwai, da kuma wani ɗan ƙasar Kanada a cikin jirgin da zai nufi filin jirgin saman Gatwick na Landan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • HKI Ta Rufe Filin Saukar Jiragen Sama Na Ben Gorion Tare Da Dauke Jiragenta  Zuwa Waje
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya
  • Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai
  • Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi
  • Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi
  • Gwamnatin Tarayya Ta Dukufa Wajen Karya Farashin Kayan Abinci – Minista
  • Mutum ɗaya ya tsira da ransa cikin 242 a hatsarin jirgin India
  • Hamas : Ziyarar ministan Isra’ila Ben-Gvir a masallacin al-Aqsa kan iya tayar da yakin addini
  • Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane