Janar Tsiga ya shafe kwanaki 40 a hannun masu garkuwa duk da biyan kuɗin fansa
Published: 18th, March 2025 GMT
Bayan shafe kwanaki 40 har yanzu waɗanda suka yi garkuwa da tsohon Shugaban Hukumar Kula da Masu Yi wa Ƙasa Hidima ta Najeriy a(NYSC), Birgediya Janar Maharazu Tsiga mai ritaya ba su sako shi ba duk da cewa an biya kuɗin fansa.
Rahotanni sun nuna cewar an biya maƙudan kuɗaɗe don ganin an sako Janar Tsiga, wanda aka yi garkuwa da shi a ranar 5 ga watan Fabrairun da ya gabata a Ƙaramar Hukumar Bakori da ke Jihar Katsina.
Wata majiya ta kusa da iyalansa ta ce bayan kai kuɗin, sai da aka shafe mako guda kafin ’yan bindigar suka sake tuntuɓar iyalansa, inda suka haɗa su ta waya, sannan kuma suka sake neman ƙarin wasu kuɗaɗe.
“Saboda wasu dalilai gaskiya ba zan faɗi adadin kuɗin da aka biya ba amma kuɗaɗe ne masu yawan gaske,” a cewar majiyar.
Da farko dai waɗanda suka yi garkuwa da tsohon Janar ɗin, sun buƙaci a ba su naira miliyan 250 a matsayin kuɗin fansa, sai dai an ci gaba ta tattaunawa da su.
Wasu bayanai na cewa akwai yiwuwar waɗanda suka yi garkuwa da shi sun sauya masa matsugunni.
Ƙungiyar Tuntuɓa ta Arewacin Najeriya ACF da kuma ta Dattijan Jihar Katsina KEF, sun buƙaci gwamnatin da kuma rundunar sojojin ƙasar, su matsa ƙaimi wajen ganin an kuɓutar da shi da sauran mutanen da aka yi garkuwa tare da su.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: garkuwa da mutane Janar Tsiga yi garkuwa da
এছাড়াও পড়ুন:
Shugabannin Kudancin Kaduna za su karrama Janar Christopher Musa
Majalisar Shugabannin Kudancin Kaduna (SKLC) ta kammala shirye-shirye domin gudanar da gagarumar tarbar ga tsohon Babban Hafsan Tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa (mai ritaya).
Za a yi bikin ne domin tunawa da kyakkyawar rawar da majalisar ta ce ya taka a aikin soja da kuma hidimarsa ga kasa.
An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aureAn shirya gudanar da bikin ne a ranar Asabar, 22 ga watan Nuwamba, 2025, a Babban Filin Wasan na garin Kafanchan, cibiyar kasuwancin Kudancin Kaduna.
A yayin taron majalisar karo na 19 da aka gudanar a Kafanchan, Shugaban SKLC, Ishaya Dare Akau, ya ce za a ba Janar Musa lambar yabo mafi girma ta majalisar wato GCSK.
Akau, ya ce wannan karramawar tana nuni da yadda Janar Musa ya wakilci Kudancin Kaduna, Jihar Kaduna, da Najeriya baki daya cikin kwarewa da cancanta, inda ya bayyana shi a matsayin jakada nagari.
A yayin taron, majalisar ta kuma kaddamar da kwamitin kula da harkokin kudi na Bikin Gargajiya na Shekara-shekara na Kudancin Kaduna (SKFEST), inda aka nada Shugaban Hukumar Haraji ta Jihar Kaduna (KADIRS), Comrade Jerry Adams, a matsayin shugaban kwamitin.
Manyan jami’an gwamnati da dama sun halarci taron karkashin jagorancin Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, Rt. Hon. Henry Danjuma Magaji, tare da Mai ba Gwamna shawara kan harkokin siyasa, Hon. Ado Dogo Audu.
Sun yi wa majalisar bayani kan muhimman shirye-shiryen gwamnati, ciki har da amincewar da gwamnatin tarayya ta bayar na farfado da aikin gina hanyar Jere–Kagarko–Jaba–Kwoi–Kafanchan, wadda Gwamna Uba Sani na jihar Kaduna ya taimaka wajen ganin tabbatuwarsa.