Janar Tsiga ya shafe kwanaki 40 a hannun masu garkuwa duk da biyan kuɗin fansa
Published: 18th, March 2025 GMT
Bayan shafe kwanaki 40 har yanzu waɗanda suka yi garkuwa da tsohon Shugaban Hukumar Kula da Masu Yi wa Ƙasa Hidima ta Najeriy a(NYSC), Birgediya Janar Maharazu Tsiga mai ritaya ba su sako shi ba duk da cewa an biya kuɗin fansa.
Rahotanni sun nuna cewar an biya maƙudan kuɗaɗe don ganin an sako Janar Tsiga, wanda aka yi garkuwa da shi a ranar 5 ga watan Fabrairun da ya gabata a Ƙaramar Hukumar Bakori da ke Jihar Katsina.
Wata majiya ta kusa da iyalansa ta ce bayan kai kuɗin, sai da aka shafe mako guda kafin ’yan bindigar suka sake tuntuɓar iyalansa, inda suka haɗa su ta waya, sannan kuma suka sake neman ƙarin wasu kuɗaɗe.
“Saboda wasu dalilai gaskiya ba zan faɗi adadin kuɗin da aka biya ba amma kuɗaɗe ne masu yawan gaske,” a cewar majiyar.
Da farko dai waɗanda suka yi garkuwa da tsohon Janar ɗin, sun buƙaci a ba su naira miliyan 250 a matsayin kuɗin fansa, sai dai an ci gaba ta tattaunawa da su.
Wasu bayanai na cewa akwai yiwuwar waɗanda suka yi garkuwa da shi sun sauya masa matsugunni.
Ƙungiyar Tuntuɓa ta Arewacin Najeriya ACF da kuma ta Dattijan Jihar Katsina KEF, sun buƙaci gwamnatin da kuma rundunar sojojin ƙasar, su matsa ƙaimi wajen ganin an kuɓutar da shi da sauran mutanen da aka yi garkuwa tare da su.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: garkuwa da mutane Janar Tsiga yi garkuwa da
এছাড়াও পড়ুন:
Taron Ashura Ya Zama Lamari Mafi Girma Da Cinkoson Jama’a, Inda Masu Ziyara Daga Sassan Duniya Suka Isa Karbala
Gangamin Ashura ya zama lamarin mafi girma da cunkoson jama’a inda tattakiin Tuwairij yake gudana tare da faɗaɗa da ba a taɓa ganin irinsa ba
Tattakin Tuwairij na bana zuwa birnin Karbala na fuskantar hallara da cunkoson jama’a da ba a taba ganin irinsa ba, inda dimbin masu ziyara daga sassan duniya ke tururuwa zuwa hubbaren Imam Husaini da kuma titunan da ke kewaye.
Mai ba da shawara ga babban sakataren cibiyar Hubbaren Imam Husain {a.s} Fadel Oz a cikin wata sanarwa da ya aikewa kafafen watsa labarai ya bayyana cewa: “A shirye-shiryen wannan juyayi, babban Sakatariyar Haramin Imam Husain (a.s) da haramin Abbas sun samar da dukkan sharuddan da suka dace don kula da masu ziyara da kuma tabbatar da jin dadinsu.
Ya kara da cewa, “Yankin da aka kebe domin gudanar da juyayin Ashura ya samu gagarumin ci gabata hanyar fadada shi, domin a shekarun da suka gabata ana ci gaba da gudanar da ayyukan da suka yi na mallakar wuraren da ke kewaye da fadada titunan da ke zuwa gare su da nufin daukar saukaka wa masu halartar taron.
Oz ya ci gaba da cewa “Hukumar ayyuka, ‘yan sanda, sassan jami’ai, da kuma cibiyoyin gwamnati sun kuma taka rawar gani wajen hada kai don tabbatar da gudanar da juyayin Ashura cikin kwanciyar hankali da lumana.”
Ya bayyana cewa, “wannan hadin gwiwa yana nuna irin kishin da hukumomin da abin ya shafa suke da shi wajen tabbatar da nasarar gudanar da juyayin Ashura a cikin yanayi na musamman na ruhi,” yana mai jaddada cewa “wadannan fadadawa da shirye-shirye suna tafiya tare da ci gaba da karuwar masu ziyara da kuma tabbatar da samun kwarewa da kwanciyar hankali a wannan babban taron addini.”