Leadership News Hausa:
2025-03-22@00:17:06 GMT

Yawan Bishiyoyin Da Aka Dasa A Kasan Kasar Sin Ya Kai Kashi 25%

Published: 12th, March 2025 GMT

Yawan Bishiyoyin Da Aka Dasa A Kasan Kasar Sin Ya Kai Kashi 25%

Yau ce ranar dasa bishiyoyi ta kasar Sin, kuma albarkacin ranar ofishin kwamiti mai kula da harkokin dasa bishiyoyi na Sin ya gabatar da sanarwar karuwar yawan bishiyoyi da Sin ta dasa, wadda ta nuna cewa, Sin ta gabatar da manyan tsare-tsaren kiyaye muhalli, don daidaita harkoki masu nasaba da hakan a shekarar 2024, inda aka samu ci gaba mai armashi a bangaren dasa bishiyoyi.

Sanarwar ta nuna cewa, a wannan shekara Sin ta dasa itatuwa hekta miliyan 4.446, da ciyayi hekta miliyan 3.224, da kuma daidaita kasa mai rairayi hekta miliyan 2.783, hakan ya sa yawan fadin gandun daji ya kai kashi 25%.

Tun lokacin da aka kira taro karo na 18 na jam’iyyar JKS, hukumar lura da itatuwa da ciyayi ta Sin ta aiwatar da manyan ayyukan dasa bishiyoyi da habaka fadin gandun daji, da kyautata ingancin itatuwa da kiyaye albakatun bishiyoyi. Yawan itatuwa da Sin ta dasa a wurare masara shuke-shuke ya kai hekta miliyan 77.33, hakan ya sa Sin ta zama kasa mafi samun ci gaba wajen dasa bishiyoyi. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: hekta miliyan

এছাড়াও পড়ুন:

An Zabi ‘Yan Kasar Zimbabwe  Kuma Mace Ta Farko A Matsayin Shugabar Shugabar Kwamitin  Wasannin Olympic

‘Yar kasar ta Zimbabwe Kiristy Coventry ta zama mace ta farko daga fito daga nahiyar Afirka,kuma mace da za ta rike shugabannin hukumar wasannin Olympic.

An zabi Kirsty  ‘yan shekaru 41 ne a yayin kada kuri’a ta sirri da aka yi da ‘yan takara 7 su ka yi gogayya. An yi zaben ne ne a yayin taron hukumar ta Olympic karo na 144, a birnin Costa, Navarino a kasar Greece a jiya 20 ga watan nan na Maris.

Gabanin zabenta dai , Kirsty ta kasance wacce ta zama gwarzuwa ta iyo har sau biyu a wasannin Olympic.

Za ta fara aikin nata ne na shugabancin hukumar wasannin Olympic  a ranar 23 ga watan Yuni, da za ta gaji Thomas Bach dan kasar Jamus.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Zabi ‘Yan Kasar Zimbabwe  Kuma Mace Ta Farko A Matsayin Shugabar Shugabar Kwamitin  Wasannin Olympic
  • Shugaban Kasar Iran Ya Bukaci Hadin Kai Tsakanin Iraniyawa Saboda Amfanin Kasar
  • NAJERIYA A YAU: Illar Sare Itatuwa Ga Sauyin Yanayi Da Lafiyarmu
  • Manufofin Kasar Sin Sun Zamo Jagora Ga Duniya A Fannin Kare Hakkokin Bil Adama
  • Kungiyar M-23 Ta Kasar Kongo Ta Kara Nusawa Gaba A Don Mamaye Karin Yankuna A Gabacin Kongo
  • Sojojin HKI Sun Kara Kisan Karin Falasdinawa 71 A Zirin Gaza
  • Amurka Ta Kai Sabbin Hare-Hare Kan Kasar Yemen Don Tallafawa HKI
  • A Jiya Laraba Ce Iran Take Bukukuwan Cika Shekaru 78 Da Kwatar Kamfanin Man Fetur Na Kasar Daga Hannun Turawan Burtaniya
  • MDD Ta Zargi Kasar Rasha Da Aikata Laifukan Yaki A Ukraine
  • Shugaban Duruz A Kasar Syria Ya Ki Amincewa Da Sabon Tsarin Mulkin Kasar