Mataimakin Firaministan Sin Ya Zanta Da Sakataren Baitulmalin Amurka
Published: 22nd, February 2025 GMT
Jagoran kula da harkokin tattalin arziki da kasuwanci na kasashen Sin da Amurka a bangaren Sin, wanda kuma shi ne mataimakin firaministan kasar Sin, He Lifeng, ya zanta da sakataren baitulmalin Amurka, Scott Bessent, ta kafar bidiyo jiya Jumma’a 21 ga wata, inda suka yi musanyar ra’ayoyi kan wasu muhimman batutuwan da suka shafi tattalin arzikin kasashen biyu, bisa matsayar da shugabannin kasashen biyu suka cimma.
Bangarorin biyu duk sun amince da muhimmancin alakokin tattalin arziki da kasuwanci a tsakaninsu, inda suka yarda su ci gaba da tuntubar juna kan batutuwan da suka fi daukar hankulansu.
Har wa yau, kasar Sin ta nuna matukar damuwa kan matakin da Amurka ta dauka kwanan nan, na kara sanya wa hajojin kasar Sin harajin kwastam. (Murtala Zhang)
এছাড়াও পড়ুন:
Amurka Tana Takurawa JMI Don Biyan Bukatun HKI Na Ta Dakatar Da Shirinta Na Nukliya
Gwamnatin kasar Amurka tana takurawa JMI ne don ta dakatar da shirinta na makamashin nukliya. Don haka ne Amurka take barazana ga Iran a kan cewa idan bata amince a cimma yarjeniya da ita a kan shirinta na makamashin Nukliya ba to ba abinda ya rage sai zabinb soje don wargwaz cibiyotyin makamashin nukliya na kasar Iran.
Wannan bukatar itace HKI ta yi ta nanatawa a MDD a kuma duk inda jami’an gwamnatinta suka yi jwabi shekara da shekaru. A halin yanzu Amurka na bin wannan Shirin sau da kafa. Wata majiya ta shaidawa tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran kan cewa, a zagayen tattaunawa har 4 wadanda kasashen biyu suka gudanar za’a fahinci cewa Amurka tana bukata a wajen Amurka fiye da abunda ta gabatar a zaman taro na farko, na biyu na uku da na hudu da suka gabata.
Sai zai don tsoron kada ta kori Iran tun ba’a je ko in aba, taki ta kawo wadannan al-amura, said ai ta bayyana su a kafafen yada labarai.
Manufar tattaunawar dai kamar yadda Amurka ta bayyana itace hana Iran mallakar makaman Nukliya. Amma sai ta bayyana bas hi bane bayan zagaye na 4, manufar itace hana Iran tace makamacin Uranium kwatakwata. Abbas Argchi ministan harkokin wajen kasar Iran ya manufar ta na shiga tattaunawa ba kai tsaye ba da Amurka it ace ganin an dauke mata takunkuman tattalin arzikin da Amurka ta dorawa kasa. Amma a tattaunawar da suka gabata Amurka bata ma kawo batun ba.