Amurka Ta Ce Zata Gabatar Da Nata Shawara Dangane Da Kawo Karshen Yakin Ukraine Ga Babban Zauren MDD
Published: 22nd, February 2025 GMT
A karon farko tun bayan fara yaki a Ukraine tsakanin Rasha da Ukraine a shekara 2022 Amurka bata taba goyon bayan wani kuduri dangane da dakatar da yaki a Ukraine a babban zauren MDD wanda Ukraine da kuma kasashen Turai suka gabatar ba.
Amma a halin yanzu ta ce zata tsara nata shawarar dangane da kawo karshen yaki a Ukraine.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio ya bayyana cewa gwamnatin Amurka zata gabatar da nata kudurin dangane da tsaida yaki a kasar Ukraine ga babban zauren MDD.
Labarin ya kara da cewa Rubio ya ce zai gabatar da kudurin ne a ranar litinin mai zuwa wato ranar 24 ga watan Fabrairu na shekara 2025 wanda itace ranar da aka fara yakin shekaru 3 da suka gabata.
Rubio ya nakalto shugaba Donaltrup yana son a gabatar da shawara wanda dukkan wakilan kasashen duniya zasu amince don kawo karshen yakin, kuma za’a sami zaman lafiya mai dorewa a yankin .
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran ta caccaki kudurin IAEA wanda ta ce yana cike da siyasa
Iran ta yi Allah-wadai da wani kuduri da ta danganta da na siyasa da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA ta dauka, tana mai cewa ba shi da tushe na fasaha ko doka.
Hukumar kula da makamashin nukiliya ta Iran (AEOI) da ma’aikatar harkokin wajen kasar sun fitar da sanarwar hadin gwiwa yau Alhamis bayan da majalisar gwamnonin hukumar ta IAEA suka amince da wani kuduri da ke zargin Iran da rashin cika alkawuran da ta dauka na nukiliya.
Kuri’u 19 ne suka amince da kudurin wanda Amurka da Birtaniya da Faransa da Jamus suka tsara.
Kasashen Rasha, China da Burkina Faso sun kada kuri’ar kin amincewa da shi, Yayin da kasashen Afirka ta Kudu, Indiya, Pakistan, Masar, Indonesia da Brazil suka ce su kam ba ruwan su.
Sanarwar da Iran ta fitar dangane da wannan kudiri ta ce, Jamhuriyar Musulunci ba ta da wani zabi face mayar da martani ga wannan kudiri na siyasa.”
Sanarwar ta ce, Shugaban Hukumar Makamashin Nukiliya ta Iran (AEOI), Mohammad Eslami, ya ba da umarnin gina sabuwar cibiyar tace uranium a wani wuri mai aminci.
Sabuwar cibiyar za ta kunshi sabbin na’urorin tace uranium na zamani inji sanarwar.
A cikin sanarwar, Tehran ta yi tir da kudirin na “siyasa da son zuciya” na IAEA Wanda Amurka da manyan kasashen Turai uku – Faransa, Jamus da Birtaniya suka tsara.
Iran ta kuma yi tir da shirun da Amurka da kawayenta na Turai suka yi wajen tinkarar yadda gwamnatin Isra’ila ke ci gaba da kin mutunta yarjejeniyar hana yaduwar makaman kare dangi.
Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da Iran da Amurka suka tabbatar da sake ganawa a karo na shida a ranar Lahadi mai zuwa game da shirin nukiliyar Iran wanda a’a gudanar a birnin Muscat a shiga stakanin kasar Oman.