Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kano ta raba kayan tallafi
Published: 22nd, February 2025 GMT
Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Kano (SEMA) da Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), sun fara raba kayayyakin tallafi ga mutum 507 da ambaliyar ruwa ta shafa a jihar a 2024.
An gudanar da rabon kayayyakin a ranar Juma’a a Ƙananan Hukumomin Kibiya da Madobi, inda Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya miƙa kayayyakin ga waɗanda suka ci gajiyar shirin.
Kwamishinan Harkokin Jin-ƙai da Rage Talauci, Alhaji Adamu Aliyu Kibiya ne, ya wakilci gwamnan.
Gwamnan, ya gode wa NEMA bisa goyon bayan da ta ke bai wa jihar, tare da yaba wa SEMA saboda jajircewarta wajen tabbatar da cewa tallafin ya isa ga waɗanda abin ya shafa.
“Muna da niyyar ci gaba da aiki tare da hukumomin da suka dace don inganta shirye-shiryen daƙile iftila’i a Kano,” in ji shi.
“Gwamnati za ta ci gaba da ƙarfafa haɗin gwiwa don kare lafiyar jama’a.”
Daraktar Janar na NEMA, Hajiya Zubaida Umar, ta ce wannan tallafi wani ɓangare ne na ƙoƙarin Gwamnatin Tarayya na taimaka wa waɗanda ambaliya ta shafa.
Ta hannun Kwamandan NEMA a Kano, Dokta Nura Abdullahi, ta bayyana cewa an amince da tallafin ne bayan Gwamnatin Tarayya ta karɓi rahoto kan ɓarnar da ambaliyar ta haifar.
“Gwamnatin Tarayya tana jajanta musu kan yanayin da suka shiga,” in ji ta.
Kayayyakin da aka raba sun haɗa da buhu 500 na shinkafa mai nauyin kilo 25, buhu 500 na masara mai nauyin kilo 25, katan 45 na tumatirin gwangwani, katan 45 na man girki, katan 45 na maggi, da buhu 20 na gishiri.
Sakataren Zartarwa na SEMA, Alhaji Isyaku Kubarachi, ya buƙaci waɗanda suka amfana da su yi amfani da kayayyakin yadda ya dace.
Wani daga cikin waɗanda suka ci gajiyar shirin, Nura Sani, ya nuna jin dadinsa.
“Wannan tallafi zai taimaka mana sosai a wannan mawuyacin lokaci. Muna godiya ga gwamnati bisa ƙoƙarinta,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
Taron kaddamar da rabar da taraktocin noman, ya gudana ne a Shalkwatar Ma’aikatar Kula da Aikin noma da kuma yin Noman Rani da ke garin Kalaba.
Kazalika, taron ya samu halartar ‘yan Majalisa da Sarakunan Gargajiya da kungiyoyin manoma mata da masu ruwa da tsaki a fannin aikin noma da ke jihar da abokan hadaka.
Daukacinsu, sun jinjina wa wannan kokari na gwamna Bassey, kan wannan hangen nesa da gwamnatinsa ta yi, na kaddamar da taraktocin noman, musamman domin ciyar da fannin aikin noman jihar gaba, duba da cewa; fannin ne kinshikin tattalin arzikin jihar.
Har ila yau, gwamna Bassey, ya nanata kudurin gwamnatinsa wajen ci gaba da bai wa fannin aikin noma muhimmanci a matsayin fannin da ke kara habaka tattalin arzikin jihar.
“A lokacin da na karbi jan ragamar shugabancin jihar, mun samar da dabaru da kuma daukar matakai daban-daban, domin kara habaka fannin,“ in ji gwamna Bassey.
“Biyo bayan wata ganawa da muka yi da manoman da ke daukacin kananan hukumominmu, mun gano cewa; kalubalen da suke fuskanta sama da kashi 70 cikin dari, na shiye-shiyen share gonakansu ne, domin fara noma su; saboda kudaden da suke kashewa masu yawa, wajen gyaran gonakin nasu, muna da yakinin wannan shirin zai magance wadannan matsaloi,” a cewar gwamnan.
Kazalika, gwamnan ya bayyana cewa; wannan rabar da taraktocin noma, wadanda ba sa shan man sosai, an tsara su ne kan yadda manoma za su yi gyaran gonakinsu cikin sauki tare kuma da rage musu kashe kudade masu yawa da kuma kara habaka fannin na aikin noma.
“Kashi 108 na kashin farko na shirin, an raba wa manoman jihar jimillar taraktocin noma 324, wadanda kuma aka rabar da su a daukacin fadin jihar,“ a cewar gwamnan.
Gwamna Bassey ya ci gaba da cewa, za a ci gaba da kula da taraktocin ne a karkashin tsarin kungiyoyin manoma na jihar.
“Hakan zai bai wa wadanda suka amfana da taraktocin damar daukar nauyin ci gaba da kula da su, wanda kuma sauran manoman da ke karkara a jihar, su ma za su samu damar samun taraktocin,” in ji shi.
“Ta wannan hanyar, za mu samu damar cin gajiyar da ke fannin noma na jihar, wanda hakan zai kuma bai wa manoman jihar kara dagewa, domin yin noma da samun kudaden shiga da kuma kara samar da wadataccen abinci a jihar,” a cewar tasa.
Kazalika, gwamnan ya kuma zayyano wasu ayyukan noma da gwamnatinsa ta kaddamar da su da suka hada da na samar da Irin noman Rogo, aikin noman Masara da na Waken Soya da sauransu.
Ya bayyana cewa, gwamnatin na kuma ci gaba da habaka samar da Irin Farin Wake da rabar da kayan aikin noma ga kananan manoma tare da kuma shirye-shiyen noman Koko (Cocoa) da Ganyen Shayi, wanda za gudanar ta hanyar yin hadaka da gwamnatin da kuma ‘yan kasuwa.
“Kaddamar da rabar da wadannan taraktocin noman, na daya daga cikin kason farko na kudurin gwamnatinmu na bunkasa fannin aikin noma na jihar, musamman ta hanyar yin amfani da kayan aikin noma na zamani,” in ji gwamnan.
Shi ma, shugaban kamfanin da ya yi kwangilar kawo taraktocin, Femi Odeshirin, ya yaba wa shirin, wanda ya ce; hakan zai kara bunkasa fannin aikin noma na jihar.
“Ba wai kawai rabar da wadannan taraktocin noma ga manoman jihar ba ne da gwamnan ya yi ba, hakan zai kuma kara inganta rayuwar manoman da suka amfana,” in ji Odeleye.
Ya bayyana cewa, kamfanin na kuma kan shirin kafa masana’antar da ake hada taraktocin noma a garin Kalaba da ke jihar, inda masana’antar za ta samar da ayyukan yi sama da 2,000.
Shi kuwa, shugaban kungiyar manoma ta kasa (AFAN) reshen jihar, Ojikpong Nyiam Bisong, danganta salon shugabancin gwamna Bassey ya yi da na marigayi tsohon Firimiyan Kudancin Nijeriya, Dakta Michael Okpara.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA