Jiniyar gargadi ta kada a cikin sassa masu yawa na Falasdinu dake karkashin mamaya  bayan harbo makami mai linzami da mutanen Yemen su ka yi.

Kafafen watsa labarun HKI sun ce, jiniyar gargadin ta kada a cikin garuruwa 255 a HKI daga cikin har da birnin Kudus.

Jaridar “Yediot Ahronot” ta buga labarin dake cewa, wasu barguzan makami mai linzamin sun fada a unguwar “Mifo Hurun”.

Har ila yau harba makami mai linzamin daga Yemen ya sa an dakatar da zirga-zirgar jirage a filin saukar jiragen sama na “Ben Gorion”.

Jaridar “Yesrael Home” ta ce miliyoyin mutane ne su ka shiga dakunan boya saboda kaucewa makami mai  linzamin da aka harbo daga Yemen.

A jiya Laraba Sayyid Abdulmalik al-Husi, jagoran kungiyar  Ansarullah ya yi alkawalin ci gaba da kai wa HKI hare-hare har zuwa lokacin da za  a kawo karshen kai wa Gaza hari, da kuma dauke takunkumin hana shigar da kayan agaji zuwa yankin.

Sayyid Abdulmalik Husi ya kuma kara da cewa, al’ummar Yemen za su ci gaba da yin duk abinda ya dace a kowane mataki domin taimaka wa al’ummar Falasdinu, ta hanyar kai wa HKI hari.

Tun a cikin watan Nuwamba na 2023 ne dai al’ummar Yemen su ka fara kai wa HKI hari a matsayin taya Falasdinawa fada, haka nan kuma sun hana duk wani jirgin ruwa mai zuwa HKI wucewa ta tekun “Red Sea”.

A gefe daya, Amurka da Birtaniya suna ci gaba da kai wa Yemen hare-hare a karkashin kare HKI da suke yi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Komai zai iya faruwa a hare-haren da za mu kai Nijeriya — Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce ƙasarsa na shirin ɗaukar matakan soja da ka iya haɗawa da hare-haren ƙasa da na sama a Nijeriya.

Trump ya bayyana haka ne yayin da yake tattaunawa da manema labarai, inda yake amsa tambayar yanayin yadda hare-haren za su kasance ta sama ko ta ƙasa.

NAJERIYA A YAU: Ko Kawo Dakarun Amurka Zai Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Najeriya? Tsagin Damagum da Anyanwu sun shirya mamaye hedikwatar PDP a yau

A cewarsa, “komai na iya faruwa, abubuwa da dama za su faru. Ina nufin abubuwa masu yawa,” in ji shi kamar yadda Kamfanin Dillancin Labarai na Reuters ya ruwaito.

Shugaban ya ƙara da cewa, “Suna kashe Kiristoci, kuma suna kashe su da yawa. Ba za mu bari hakan ta ci gaba da faruwa ba.”

A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta a ranar Asabar, Trump ya bayyana cewa ya umarci Ma’aikatar Tsaron Amurka ta Pentagon da ta tsara yiwuwar kai hari kan Najeriya.

Wannan na zuwa ne kwana guda bayan ya yi gargaɗin cewa Kiristoci na fuskantar kisan kiyashi a ƙasar.

Sai dai gwamnatin Najeriya ta ce tana kallon wannan batu a matsayin lamarin da za a iya warwarewa ta hanyar diflomasiyya, tana mai cewa ƙasashen biyu abokan hulɗa ne wajen yaƙi da ta’addanci.

Cikin wani saƙo da mai magana da yawun fadar gwamnatin Nijeriya Daniel Bwala ya wallafa ranar Lahadi, ya ce idan shugabannin ƙasashen biyu suka gana, akwai fatan samun mafita mai kyau.

Barazanar Trump

A wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Truth Social da tsakiyar daren ranar Asabar, Donald Trump ya ce Amurka za ta dakatar da dukkan tallafin da take bai wa Nijeriya nan take idan har gwamnati ta ci gaba da nuna halin ko in kula kan kisan da ake yi wa mabiya addinin Kirista a kasar.

Hakazalika, Trump ya ce Amurka na iya kutsa wa Nijeriya da ƙarfin soji domin kakkabe ’yan ta’adda masu aikata ta’asa da sunan addinin Islama, sannan ya umurci Ma’aikatar Yaƙi ta Amurka da ta shirya domin yiwuwar kai wa Nijeriya samame.

Wannan furici na Trump na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnatinsa ta saka Najeriya a jerin ƙasashen da ake yi wa Kirista kisan ƙare dangi, zargin da fadar mulki ta Abuja ta musanta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zamfara Ta Tashi Daga Matsayi Na 36 Zuwa Na 17 A Shekara Biyu Ƙarƙashin Gwamna Lawal — Rahoton BudgIT
  • Komai zai iya faruwa a hare-haren da za mu kai Nijeriya — Trump
  • Al’ummar Kauru Sun Koka Game Da Karuwar Hare-hare Da Ke Barazana Ga Gonaki Da Rayuka
  • Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Jamus ta shiga sahun ƙasashen da ke neman kawo ƙarshen yaƙin Sudan
  • Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya
  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi