HausaTv:
2025-07-31@17:57:18 GMT

 Sojojin Iran: Gwagwarmaya Ce Kadai Hanyar Warware Matsalar Falasdinu

Published: 27th, March 2025 GMT

Sojojin Iran sun fitar da bayani a daidai lokacin da ake shirin  raya ranar Kudus ta duniya, suna masu bayyana cewa; Hanyar da za ta warware matsalar Falasdinu ita ce yin gwgawarmaya da kuma samun goyon baya daga al’ummun duniya.

Bayanin ya kuma kara da cewa; A daidai lokacin da al’ummar Falasdinu suke fuskantar zalunci,ta’addanci, da amfani da karfi a kansu, da kuma yin barna a masallacin Kudus, da majami’u, makarantu, asibitoci da kuma cibiyoyin MDD, da kuma shiru din da duniya ta yi, hakan yana nufin cewa ‘yan sahayoniya masu aiki da duk wata ka’ida ko doka ta kasa da kasa balle kuma halayyar kwarai, a dalilin hakan, hanya daya tilo da za a iya sauya wannan yanayin shi ne ci gaba da gwgawarmaya, sannan kuma da samun goyon bayan al’ummar duniya.

Bayanin ya ci gaba da cewa; A wannan lokacin na jajiberin ranar Kudus,al’ummar Falasdinu suna cikin mawuyacin yanayi na cin zali da nuna karfi akansu da ‘yan sahayoniya suke yi ta hanya mafi muni, da hakan ya yi sanadiyyar shahadar dubban Falasdinawa da kuma jikkatar wasu dubu dubatar, daga cikinsu da akwai kananan yara, mata da kuma fararen hula.”

Bayanin sojojin na Iran ya yi kira ga dukkanin ‘yantattun mutane a duniya da su fito domin nuna goyon bayansu ga al’ummar Falasdinu da ake cin zalinsu, tare da kara da cewa, al’ummar Iran ma’abota juyin juya hali za su fito a ranar Kudus ta duniya domin nuna kin jinin zalinci irin na ‘yan sahayoniya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Muddin Isra’ila ba ta cika wasu sharuɗa ba za mu amince da kafa ƙasar Falasɗinu — Birtaniya

Birtaniya ta sanar da cewa muddin Isra’ila ba ta biyayya wa wasu sharuɗa ba, to kuwa a watan Satumba mai zuwa za ta amince da Falasɗinu a matsayin halastacciyar ƙasa a yayin taron Babban Zauren Majalisar Ɗinkin Duniya (UNGA).

Firaiministan Birtaniya Keir Starmer ne ya bayyana haka a wani jawabi da ya gudanar a yau Talata.

Starmer ya ce za su amince da ‘yancin Falasɗinu idan har Isra’ila ba ta ɗauki hanyar kawo ƙarshen halin da ake ciki a Gaza ba, ciki har da tsagaita wuta da kuma tsarin samar da zaman lafiya na din-din-din.

Nijar da Rasha sun ƙulla yarjejeniyar makamashin nukiliya Remi Tinubu ta bai wa waɗanda harin Benuwe ya shafa tallafin Naira biliyan ɗaya

A cewarsa, hakan zai tabbata “har sai idan Isra’ila ta ɗauki matakai na kawo karshen abin da ke faruwa a Gaza, ta cimma yarjejeniyar tsagaita wuta, ta kuma tabbatar da cewa ba za a ƙwace Gaɓar Yamma ba, har ma da cimma yarjejeniyar zaman lafiya ta tsawon lokaci da za ta haifar da mafitar ƙasashe biyu.”

Firaministan ya ƙara nanata cewa babu wani bambanci tsakanin Isra’ila da Hamas kuma buƙatar da Birtaniya take da su kan Hamas suna nan — cewa dole su saki dukkan waɗanda suke garkuwa da su, su saka hannu kan yarjejeniyar tsagaita wuta, su kuma amince cewa ba za su saka baki a gwamnatin Gaza ba sannan su ajiye makamai.

Starmer ya ce za su ci gaba da duba lamarin da ke faruwa a Gaza gabanin taron babban zauren MDD da za a yi don ganin yadda ɓangarorin biyu suka ɗauki matakai na samar da zaman lafiya kafin ta ɗauki mataki na karshe.

Matakin da Birtaniyar ke shirin dauka na zuwa ne biyo bayan matsin lamba da Starmer ke sha a cikin ƙasar, inda ‘yan majalisu sama da 200 a makon da ya wuce, suka buƙaci ya aminta da ‘yancin Falasɗinu.

Baya ga haka kuma, ɗaruruwan mutane sun gudanar da zanga-zanga a titunan birnin Landan, suna mai kira ga Starmer ya amince da buƙatarsu na a samar da ƙasar Falasɗinu.

Ƙasashe da dama, kusan 139 sun amince da Falasɗinu a matsayin ƙasa a hukumance, kuma a makon da ya wuce Faransa ta ce za ta yi shelar hakan yayin taron na Majalisar Ɗinkin Duniya da ke gudana yanzu haka.

Rikicin Gabas ta Tsakiya na ƙara ƙamari, inda al’ummar Gaza ke mutuwa a kullum , yayin da suke fuskantar matsananciyar yunwa, abinda wasu ke ganin samar da ƙasar Falasɗinu ne na mafita domin kawo ƙarshen yaƙin baki ɗaya.

A halin yanzu ƙasashen duniya sama da 100 ne ke tattauna makomar Falasdinu a taron Majalisar Ɗinkin Duniya.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana cewa matsalar yunwa mafi muni a duniya na shirin faruwa a Gaza, saboda yadda mutane ke mutuwa wasu ke galabaita a dalilin rashin abinci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Sojojin Sahayoniya Suna Ci Gaba Da Kisan Kiyashi A Gaza
  • Tawagar Iran Ta Fice A Taron Majalisun Dokokin Kasashen Duniya A Lokacin Jawabin Wakilin Isra’ila
  • Shugabannin Arewa Sun Tattauna Sabon Hanyar Ci Gaba – Minista Uba Maigari Ya Yaba
  • Majalisa ta ba NNPCL mako uku ya yi mata bayanin inda tirilyan 210 ta shiga
  • MDD Zata Aiwatar Da Hanyar Warware Rikicin Falasdinawa Da Yahudawan Sahayoniyya
  • Muddin Isra’ila ba ta cika wasu sharuɗa ba za mu amince da kafa ƙasar Falasɗinu — Birtaniya
  • Jagora: Iran Ta Bayyana Karfinta Da Jajircewarta A Yakin Kwanaki 12 Ga Duniya
  • Sojojin HKI Sun Ci Gaba Da Kashe Kawunansu
  • Kasar Iran Ta Musanta Yin Katsalandan A Tattaunawar Neman Tsagaita Bude Wuta A Gaza
  • Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa