Adadin ‘yan jarida wadanda suka yi shahada a Gaza ya karu zuwa 226 tun bayan fara kisan kare dangi kan yankin

Ofishin yada labarai na gwamnati a Gaza ya tabbatar a yau Juma’a cewa: Adadin ‘yan jaridun da suka yi shahada ya karu zuwa 226, bayan sanar da shahadar dan jarida Ahmed Qaljah.

Ofishin ya bayyana cewa: Yawan ‘yan jaridan da suka yi shahada ya karu zuwa 226 tun farkon yakin kisan kare dangi kan zirin Gaza, bayan sanar da shahadar daya daga cikin ‘yan jaridan Falasdinawa: Ahmed Qaljah, wanda ya yi aiki a matsayin mai daukar hoto na gidan talabijin na Al-Arabiya.

Ofishin ya yi Allah-wadai da kakkausar murya kan yadda gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ke kai hare-haren wuce gona da iri da kashe-kashen kare dang ikan al’ummar Falasdinu da kuma kashe ‘yan jaridar Falasdinawa. Don haka ta jadada yin kira ga kungiyar ‘yan jarida ta kasa da kasa, kungiyar ‘yan jarida ta Larabawa, da dukkanin kungiyoyin ‘yan jaridu a duniya da su yi Allah wadai da wadannan laifuffuka na yau da kullun kan ‘yan jarida a Falasdinu wadanda suka kasance kwararrun kafafen yada labarai a zirin Gaza.

Ofishin yada labarai na gwamnati ya dora laifukan kisan kare dangin kan gwamnatin mamayar Isra’ila, gwamnatin Amurka, da kasashen da ke da wasu kasashen Turai musamman kasashen Birtaniya, Jamus, da Faransa, da alhakin aikata wadannan munanan laifuka.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Namadi Ya Amince Da Nadin Sabbin Sakatarori Guda Takwas

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya amince da nadin sabbin manyan  sakatarori  guda takwas, da kuma mayar da wasu hudu zuwa wasu ma’aikatu, da hukumomi da sassan gwamnati daban-daban.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da shugaban ma’aikatan jihar, Alhaji Muhammad K. Dagaceri, ya fitar a Dutse, inda ya bayyana cewa daga cikin sabbin sauye-sauyen akwai Sagir Muhammad Sani daga Ma’aikatar Ilimin Firamare zuwa Ma’aikatar Tsare-tsare da Tattalin Arziki, da kuma Muhammad Yusha’u daga Ma’aikatar Tsare-tsare da Tattalin Arziki zuwa Ma’aikatar Harkokin Kananan Hukumomi.

Sai Lawan Muhammad Haruna daga Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi zuwa Hukumar Kula da Ayyukan Kananan Hukumomi, da kuma Injiniya Musa Alhassan Arobade daga Ma’aikatar Wuta da Makamashi zuwa Hukumar Bunƙasa Ma’aikata da Horaswa, wadda ke ƙarƙashin ofishin Shugaban Ma’aikata na Jiha.

Alhaji Muhammad Dagaceri ya bayyana cewa, sabbin sakatarorin da aka nada su ne Garba D. Muhammad zuwa Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi, da Kimiyya da Fasaha, da Fatima Aliyu Hadejia zuwa Hukumar Albashi da Fansho ƙarƙashin ofishin Shugaban Ma’aikata.

Sauran sun haɗa da Baffa Abubakar wanda aka tura zuwa Ma’aikatar Ilimin Firamare, sai Bello Datti zuwa Sashen Kula da Harkokin Musamman/Al’amuran Majalisar Zartarwa ƙarƙashin ofishin Sakataren Gwamnatin Jihar Jigawa, da Ibrahim Hassan zuwa Ma’aikatar Kuɗi, da kuma Nasiru Haruna zuwa Ma’aikatar Wuta da Makamashi, sai Umar Isah zuwa Hukumar Kula da Ma’aikata, yayin da Mahmud Isah Ringim aka tura shi zuwa Ma’aikatar Kasuwanci da Masana’antu.

Shugaban Ma’aikatan ya ƙara da cewa, wannan sauyin zai fara aiki ne nan take.

 

Usman Muhammad Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ummar Fegin Mahe Sun Yi Zanga-zanga Kan Kisan Jama’a Da ‘Yan Bindiga Ke Yi
  • A Kalla Falasdinawa 10 Yunwa Ta Kashe A Gaza A Cikin Sa’o’i 24
  • Gwamna Sule Ya Ƙara Musanta Zargin Kare Ƴan Ta’adda A Nasarawa
  • Gwamna Namadi Ya Amince Da Nadin Sabbin Sakatarori Guda Takwas
  • Tinubu Ba Zai Taɓa Tauye ’Yancin Kafafen Yaɗa Labarai Ba, In ji Ministan Yaɗa Labarai
  • Sheikh Qasem: Nuna Halin Ko In-Kula Na Duniya Ne Ya Jawo Kisan Kiyashi A Gaza
  • Kasar Sin Tana Da Dokoki Da Ka’idoji Sama Da 180 Dake Kare Nakasassu
  • Fizishkiyan: Batun Kare Hakkin Bil’adama Ba Komai Ba Ne Sai Karya
  • Mutum 16 sun mutu a haɗarin jirgin sama a Bangladesh
  • Kungiyar Hamas Ta Yi Suka Kan Kame ‘Yan Gwagwarmaya Da Hukumar Falasdinawa Ke Yi