Adadin ‘Yan Jaridar Falasdinu Da Suka Yi Shahada Sun Karu Zuwa 226 Tun Bayan Fara Kisan Kare Dangi A Gaza
Published: 6th, June 2025 GMT
Adadin ‘yan jarida wadanda suka yi shahada a Gaza ya karu zuwa 226 tun bayan fara kisan kare dangi kan yankin
Ofishin yada labarai na gwamnati a Gaza ya tabbatar a yau Juma’a cewa: Adadin ‘yan jaridun da suka yi shahada ya karu zuwa 226, bayan sanar da shahadar dan jarida Ahmed Qaljah.
Ofishin ya bayyana cewa: Yawan ‘yan jaridan da suka yi shahada ya karu zuwa 226 tun farkon yakin kisan kare dangi kan zirin Gaza, bayan sanar da shahadar daya daga cikin ‘yan jaridan Falasdinawa: Ahmed Qaljah, wanda ya yi aiki a matsayin mai daukar hoto na gidan talabijin na Al-Arabiya.
Ofishin ya yi Allah-wadai da kakkausar murya kan yadda gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ke kai hare-haren wuce gona da iri da kashe-kashen kare dang ikan al’ummar Falasdinu da kuma kashe ‘yan jaridar Falasdinawa. Don haka ta jadada yin kira ga kungiyar ‘yan jarida ta kasa da kasa, kungiyar ‘yan jarida ta Larabawa, da dukkanin kungiyoyin ‘yan jaridu a duniya da su yi Allah wadai da wadannan laifuffuka na yau da kullun kan ‘yan jarida a Falasdinu wadanda suka kasance kwararrun kafafen yada labarai a zirin Gaza.
Ofishin yada labarai na gwamnati ya dora laifukan kisan kare dangin kan gwamnatin mamayar Isra’ila, gwamnatin Amurka, da kasashen da ke da wasu kasashen Turai musamman kasashen Birtaniya, Jamus, da Faransa, da alhakin aikata wadannan munanan laifuka.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi
A cewarsa, jami’an tsaron sun samu kiran gaggawa da ke cewa, wasu gungun ‘yan fashi da makami sun rufe babbar hanyar, sun fara yin fashi ga matafiya a ranar 4 ga watan Yunin 2025.
Nan take aka tura tawaga a ƙarƙashin jagorancin babban jami’in ɗansanda (DPO) da ke kula da caji ofis ɗin Toro, tare da haɗin guiwar sauran jami’an tsaro inda suka nufi wurin da nufin daƙile fashin.
Da isarsu wurin, suka fara musayar wuta inda jami’an tsaron suka samu nasarar fatattakarsu wanda hakan ya janyo da dama daga cikin ‘yan fashin suka gamu da raunuka na harbin bindiga sannan an harbe daya ya mutu nan take.
LEADERSHIP ta rawaito cewa, an miƙa gawar Shagari ga sashin da ke kula da gawarwaki domin birne shi kamar yadda aka tanada.
Wakil ya ƙara da cewa, ana ci gaba da gudanar da bincike domin ganin an bi sawun sauran waɗanda ake zargin ‘yan fashi da makamin ne da suka tsere domin tabbatar da an kamo su.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp