Iran Ta Musanta Zargin Amurka Kan Cewa Kungiyoyi Masu Fada Ha HKI Suna Daukar Umurni Daga Wajenta Ne
Published: 6th, June 2025 GMT
Jakadan kasar Iran a MDD Amir Sa’eid Iravani ya musanta zargin kasar Amurka na cewa falasdinawa dauke da makamai a Gaza suna aiki ne tare da umurnin Iran. A kuma dukkan yankunan da HKI take mamaye da su a kasar Falasdinu da ta mamaye.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ya nakalto Iran vani yana cewa Amurka ta dorawa iran wannan zargin ne saboda boye laifukan yakin da HKI take aikatawa a Gaza da kuma sauran yankunan Falasdinawa da take mamaye da su.
A wani jawabin da ta gabatar a gaban kwamitin tsaro na MDD a ranar Laraba mai rike da mukamin jakadan Amurka a MDD Dorothy Shea ta bayyanawa kwamitin tsaro kan cewa dole kungiyar Hamas ta mika makamanta sannan da ita da sauran Falasdinawa su bar Gaza su je inda suka ga dama.
Bayan jawabinta ne Iravani ya rbutawa babban sakataren MDD da kuma shugaban kwamitin tsaro na wannan wato Carolyn Rodrigues-Birkett wasika inda yake musanta zarge zargen na Amurka.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Trump ya fitar da Amurka daga UNESCO saboda amincewa da Falasdinu a matsayin Mamba
Amurka ta yanke shawarar ficewa daga hukumar kula da ilimi da kimiya da al’adu ta Majalisar Dinkin Duniya UNESCO a karo na biyu saboda matakin da ta dauka na shigar da Falasdinu a matsayin mamba.
Mataimakiyar sakatariyar yada labaran fadar White House Anna Kelly ta sanar da matakin a cikin wata sanarwa a ranar Talata.
Kelly ta ce dalilin da ya suka dauki wannan kan hukumar UNESCO, shi ne ta tallafa wa shirye-shiryen da Amurka ke kallonsu a matsayin wadanda ba su dace da muradunta ba.
“Shugaba Trump ya yanke shawarar janye Amurka daga UNESCO, wadda ke kula da ayyuka a bangaren raya al’adu da ilimi da zamantakewar al’umma, saboda daukar wau matakai wadanda ba su dace da manufofin Amurka ba,” in ji Kelly.
Ta ci gaba da cewa, shigar da Falasdinu a matsayin mamba a hukumar UNESCO, Amurka na Kallon hakan a matsayin babbar matsala kuma ya saba wa manufofin Amurka, wanda hakan ke ke kara haifar da karuwar kalaman kyama ga Isra’ila a cikin kungiyar.
Darakta-janar na UNESCO, Audrey Azoulay, ya bayyana matukar Rashin jin dadinsa kan matakin da Trump ya dauka na ficewa daga kungiyar, amma ya kara da cewa dama tuni aka yi hasashen haka, kuma UNESCO ta shirya ma hakan, tare da yin nuni da cewa hukumar ta dauki matakin karkata hanyoyin samar da kudadenta, inda kusan kashi 8% na kasafin kudin ta ke fiowa daga Washington.