Aminiya:
2025-06-06@20:56:25 GMT

Mun gurfanar da mutum 29 a kotu kan zargin kashe DPO a Kano – ’Yan sanda

Published: 6th, June 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sanda ta jihar Kano ta ce ta gurfanar da mutum 29 da ta kama bisa zarginsu da hannu a kashe DPO na garin Rano da ke jihar, CSP Baba Ali da sauran laifuffuka.

Kakakin rundunar a jihar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa ranar Alhamis, inda ya ce an gurfanar da su ne a gaban kotun majistare mai lamba 20 da ke Nomansland a Kano.

Gurfanarwar dai ta biyo bayan kammala bincike kan kisan wanda ya ja hankalin mutane a ciki da wajen jihar.

NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Suka Fara Bacewa Yayin Bukukuwan Sallah Sojoji sun dakile hare-haren ‘Yan Boko Haram biyu a Borno

Kiyawa ya ce 14 daga cikin mutanen, da suka hada da Bala Yusuf, Bala Mohammed, Abdulrashid Ibrahim, Abdullahi Salisu Kere, Sadiq Buhari, Yunusa Adamu, Musa Minkaila, Mamuda Mohammed, Ismail Mamuda, Usman Shu’aibu, Musa Hassan Black, Abdulrashid Munkail, Umar Ado Nadada da Sabitu Abubakar, dukkansu ’yan asalin karamar hukumar ta Ranon ne, kuma ana zarginsu da aikata kisan kai da sauran laifuffuka.

Sauran laifuffukan da ake zargin nasu da su sun hada da hadin baki, tayar da zaune tsaye, kone-kone, ketare iyaka, jikkatawa da kuma sata.

Ragowar mutum 15 din kuma wadanda su ma aka dauki bayansu a lokacin bincike ana zarginsu da hadin baki da tayar da zaune tsaye da kuma iza wutar rikici kan kisan DPOn da kuma lalata gini.

Rahotanni dai sun bayyana yadda aka kasha marigayi CSP Baba Ali a Rano, bayan mutanen gari sun zarge shi da hannu a kashe wani wanda aka tsare a ofishin ’yan sanda.

“Rundunarmu tana ba mutane tabbacin cewa za a yi adalci a wannan shari’ar, sannan tana godiya kan sakonnin ta’aziyya da addu’o’i da taimako da kuma fahimta da hadin kan da mutane suka bayar a lokacin da ake binciken,” in ji sanarwar.

Kiyawa ya kuma ce duk da an fara shari’ar wadanda suka zo hannu, rundunar ta sha alwashin gani ta ci gaba da farautar duk ragowar masu hannu a cikin aika-aikar domin ganin su ma sun girbi abin da suka shuka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Rano

এছাড়াও পড়ুন:

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

A watan Oktoban 2024, wani jirgin ruwa ya kife da kusan mutum 300 a Mokwa, na Jihar Neja.

Haka kuma, a watan Satumban 2023, mutum 24 sun mutu a wani hatsarin kwale-kwale a Jihar Neja.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Adadin ‘Yan Jaridar Falasdinu Da Suka Yi Shahada Sun Karu Zuwa 226 Tun Bayan Fara Kisan Kare Dangi A Gaza
  • Wani mutum ya mutu a cikin rijiya a Kano
  • Sallah: ’Yan sanda sun yi alƙawarin tabbatar da tsaro a Gombe
  • Kotu ta aike da ɗan Tiktok gidan yari kan yin shigar mata a Kano
  • Sallah: Mun shirya samar da tsaro a Yobe — ’Yan Sanda
  • Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 
  • Rundunar ‘Yan Sanda A Kano Ta Haramta Bukukuwan Hawan Sallah A Kano
  • ’Yan sanda sun sake hana hawan Sallah a Kano
  • Hatsarin kwale-kwale ya yi ajalin mutum 7 a Sakkwato