Mun gurfanar da mutum 29 a kotu kan zargin kashe DPO a Kano – ’Yan sanda
Published: 6th, June 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sanda ta jihar Kano ta ce ta gurfanar da mutum 29 da ta kama bisa zarginsu da hannu a kashe DPO na garin Rano da ke jihar, CSP Baba Ali da sauran laifuffuka.
Kakakin rundunar a jihar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa ranar Alhamis, inda ya ce an gurfanar da su ne a gaban kotun majistare mai lamba 20 da ke Nomansland a Kano.
Gurfanarwar dai ta biyo bayan kammala bincike kan kisan wanda ya ja hankalin mutane a ciki da wajen jihar.
NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Suka Fara Bacewa Yayin Bukukuwan Sallah Sojoji sun dakile hare-haren ‘Yan Boko Haram biyu a BornoKiyawa ya ce 14 daga cikin mutanen, da suka hada da Bala Yusuf, Bala Mohammed, Abdulrashid Ibrahim, Abdullahi Salisu Kere, Sadiq Buhari, Yunusa Adamu, Musa Minkaila, Mamuda Mohammed, Ismail Mamuda, Usman Shu’aibu, Musa Hassan Black, Abdulrashid Munkail, Umar Ado Nadada da Sabitu Abubakar, dukkansu ’yan asalin karamar hukumar ta Ranon ne, kuma ana zarginsu da aikata kisan kai da sauran laifuffuka.
Sauran laifuffukan da ake zargin nasu da su sun hada da hadin baki, tayar da zaune tsaye, kone-kone, ketare iyaka, jikkatawa da kuma sata.
Ragowar mutum 15 din kuma wadanda su ma aka dauki bayansu a lokacin bincike ana zarginsu da hadin baki da tayar da zaune tsaye da kuma iza wutar rikici kan kisan DPOn da kuma lalata gini.
Rahotanni dai sun bayyana yadda aka kasha marigayi CSP Baba Ali a Rano, bayan mutanen gari sun zarge shi da hannu a kashe wani wanda aka tsare a ofishin ’yan sanda.
“Rundunarmu tana ba mutane tabbacin cewa za a yi adalci a wannan shari’ar, sannan tana godiya kan sakonnin ta’aziyya da addu’o’i da taimako da kuma fahimta da hadin kan da mutane suka bayar a lokacin da ake binciken,” in ji sanarwar.
Kiyawa ya kuma ce duk da an fara shari’ar wadanda suka zo hannu, rundunar ta sha alwashin gani ta ci gaba da farautar duk ragowar masu hannu a cikin aika-aikar domin ganin su ma sun girbi abin da suka shuka.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
A wani bidiyo daban da PUNCH Metro ta gani a Facebook, wanda Mc Pee ya wallafa, wani mutum da ake zargin dalibi ne na jami’ar ya bayyana abin da ya faru.
A cewarsa, marigayin ya roki a bar shi ya rayu kafin daga bisani wanda ake zargin ya kashe shi.
Ya ce: “Nanpon ya riga ya yanke Peter a kumatunsa yayin da yake rokon a bar shi. Lokacin da muka shiga tsakani muka ce ya daina, sai ya yi barazanar yanka duk wanda ya kusanto shi.
“Da Peter ya ga ba ya sauraron rokonsa, sai ya rungume shi yana rokonsa da kuka.
“Mun fita neman taimako amma babu wanda ya amsa mana. Da Peter ya yi kokarin tserewa sai ya fadi, Nanpon ya kamo shi ya ci gaba da saransa da adda.”
Wani kwararren masanin tsaro da yaki da ta’addanci ya wallafa a dandalin D a ranar Lahadi cewa jami’an rundunar ‘yan sandan Jihar Filato sun kama wanda ake zargin.
Ya kuma ambaci majiyoyi da suka tabbatar da faruwar lamarin ta hanyar rahoton da aka samu daga Babban Jami’in Tsaro na jami’ar.
Ya rubuta cewa, “Rundunar ‘Yansanda ta Filato ta kama wani dalibi mai shekaru 23 na Jami’ar Jos bisa zargin kashe abokinsa sannan ya binne shi a rami mara zurfi a cikin dakinsa da ke kauyen Rusau a Karamar Hukumar Jos ta Arewa.
“Majiyoyi sun tabbatar da faruwar lamarin a ranar Lahadi a Jos, inda suka danganta da rahoton da aka samu daga Babban Jami’in Tsaron jami’ar.
“A cewar majiyoyin, wanda ake zargin mai suna Dabid Nanpon Timmap, dalibi a matakin shekara ta uku a jami’ar, ya kai wa Peter Mata Mafurai, mai shekaru 22, hari da adda, ya kashe shi a gidansa.”
Zagazola ya kara da cewa, bayan samun kiran gaggawa da misalin karfe 9:30 na safiya, DPO na sashin Laranto ya jagoranci tawagar ‘yansanda zuwa wurin, inda aka kama wanda ake zargin.
“Majiyoyin sun ce bincike ya nuna cewa wanda ake zargin ya binne mamacin a cikin rami mara zurfi da ya haka a cikin dakinsa. An tono gawar kuma an kai ta dakin ajiye gawarwaki na Asibitin koyarwa na Jami’ar Bingham domin yin binciken gawar (autopsy),” in ji shi.
Ya kara da cewa, an tsare wanda ake zargin yayin da ake ci gaba da bincike domin gano hakikanin dalilin kashe abokin nasa.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA