Aminiya:
2025-07-25@01:57:48 GMT

Mun gurfanar da mutum 29 a kotu kan zargin kashe DPO a Kano – ’Yan sanda

Published: 6th, June 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sanda ta jihar Kano ta ce ta gurfanar da mutum 29 da ta kama bisa zarginsu da hannu a kashe DPO na garin Rano da ke jihar, CSP Baba Ali da sauran laifuffuka.

Kakakin rundunar a jihar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa ranar Alhamis, inda ya ce an gurfanar da su ne a gaban kotun majistare mai lamba 20 da ke Nomansland a Kano.

Gurfanarwar dai ta biyo bayan kammala bincike kan kisan wanda ya ja hankalin mutane a ciki da wajen jihar.

NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Suka Fara Bacewa Yayin Bukukuwan Sallah Sojoji sun dakile hare-haren ‘Yan Boko Haram biyu a Borno

Kiyawa ya ce 14 daga cikin mutanen, da suka hada da Bala Yusuf, Bala Mohammed, Abdulrashid Ibrahim, Abdullahi Salisu Kere, Sadiq Buhari, Yunusa Adamu, Musa Minkaila, Mamuda Mohammed, Ismail Mamuda, Usman Shu’aibu, Musa Hassan Black, Abdulrashid Munkail, Umar Ado Nadada da Sabitu Abubakar, dukkansu ’yan asalin karamar hukumar ta Ranon ne, kuma ana zarginsu da aikata kisan kai da sauran laifuffuka.

Sauran laifuffukan da ake zargin nasu da su sun hada da hadin baki, tayar da zaune tsaye, kone-kone, ketare iyaka, jikkatawa da kuma sata.

Ragowar mutum 15 din kuma wadanda su ma aka dauki bayansu a lokacin bincike ana zarginsu da hadin baki da tayar da zaune tsaye da kuma iza wutar rikici kan kisan DPOn da kuma lalata gini.

Rahotanni dai sun bayyana yadda aka kasha marigayi CSP Baba Ali a Rano, bayan mutanen gari sun zarge shi da hannu a kashe wani wanda aka tsare a ofishin ’yan sanda.

“Rundunarmu tana ba mutane tabbacin cewa za a yi adalci a wannan shari’ar, sannan tana godiya kan sakonnin ta’aziyya da addu’o’i da taimako da kuma fahimta da hadin kan da mutane suka bayar a lokacin da ake binciken,” in ji sanarwar.

Kiyawa ya kuma ce duk da an fara shari’ar wadanda suka zo hannu, rundunar ta sha alwashin gani ta ci gaba da farautar duk ragowar masu hannu a cikin aika-aikar domin ganin su ma sun girbi abin da suka shuka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Rano

এছাড়াও পড়ুন:

Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

Babbar Kotun Tarayya da ke Bauchi ta yanke hukunci a kan gwamnatin jihar Bauchi da ta biya tsohon Akanta-Janar na jihar, Dakta Sa’idu Abubakar, Naira miliyan 100 a matsayin diyyar take masa haƙƙi da kuma tsare shi ba bisa ƙa’ida ba. Kotun ta kuma umarci gwamnati ta wallafa ban haƙuri a manyan jaridu guda biyu cikin kwanaki 14.

Mai Shari’a Aminu Garba ya yanke wannan hukunci ne a ƙarar da Dakta Abubakar ya shigar, yana zargin gwamnati da jami’anta da take masa haƙƙi, da kama shi ba tare da bin ƙa’ida ba, da musgunawa. Ya bayyana cewa hakan ya saɓawa tanade-tanaden kundin tsarin mulki da kuma yarjejeniyar kare haƙƙin bil’adama ta Afrika.

Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Ƴansanda Sun Kama Shahararren Ɗan Damfarar Yanar Gizo A Bauchi

Waɗanda kotun ta bayyana da laifi sun haɗa da shugaban ƴansanda na ƙasa, kwamishinan ƴansanda na Bauchi, gwamnatin jihar Bauchi, Antoni Janar na jihar da hukumar karɓar ƙorafe-ƙorafe ta jihar. Kotun ta tsame hukumar DSS daga cikin hukuncin, saboda babu isasshen hujja kan rawar da ta taka.

A ƙarshe, kotun ta hana duk wani ƙarin cin mutunci, tsarewa ko kama Dakta Abubakar ba tare da bin doka ba. Haka kuma ta jaddada cewa ya cancanci diyya saboda hana shi walwala da damuwa da aka jefa shi ciki daga ranar 9 zuwa 25 ga Disamba, 2024.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ruwa da iska sun kashe mutum 5, sun raba sama da 5,000 da muhallansu a Yobe
  • Ruwa da iska sun kashe mutum, sun raba sama da 5,000 da muhallansu a Yobe
  • Zamfarawa sun yi zanga-zanga kan kisan sama da mutum 100
  • Zamfarawa sun yi zanga-zanga kan kisan mutum sama da 100
  • Uwa ta kashe ’ya’yan cikinta biyu saboda kuncin rayuwa
  • Gwamna Namadi Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Hukumar Hisba Ta Jihar Jigawa
  • Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100
  • Zazzaɓin Lassa ya kashe mutum 151 a Nijeriya bana — NCDC
  • Kotu Ta Dage Shari’ar Zargin Cin Hanci Da Ake Yi Wa Shugaban KANSIEC Na Kano Zuwa Nuwamba
  • Tsoffin Jami’an ‘Yan Sanda Sun Bukaci A fitar Da Su Daga Cikin Shirin Fansho