Ya ce an samu yawan mace-macen ne saboda rashin bin umarnin gargadin ambaliyar ruwa daga mutane a jihar.

Ya bukaci jihohi su dauki matakai don hana mummunar ambaliyar ruwa da ka iya lalata rayuka da kadarori, ministan ya ce, “Ma’aikatar Tarayya ta Albarkatun Ruwa da Tsabtace Muhalli tana mika ta’aziyya ga gwamnatin da al’ummar Jihar Neja, musamman ga al’ummomin da lamarin ya shafa a Mokwa, wadanda suka fuskanci asara, mutuwa da canjin wuri sakamakon wannan bala’i na ambaliyar ruwa.

“Ina jaddada cewa ambaliyan da aka samu ba ta kasance saboda sakin ruwa daga dam din Kainji ko Jebba ba ne, domin duka dam din suna cikin tsaro.

“Mun yaba da kokarin gaggawa na gwamnatin Jihar Neja da hukumomin yankin, da masu ba da agajin gaggawa da ke aiki ba tare da gajiya ba don bayar da taimako da goyon baya ga wadanda abin ya shafa.

“Ambaliyar ruwan da ta faru a garin Mokwa, ya samo asali ne daga ruwan sama mai yawa sakamakon yanayi mai tsanani, wanda canjin yanayi ya jawo, wani abu da ke tasowa a duniya, wanda ya shafi hanyoyin kwalbatin na yankin.

“Bugu da kari, gine-gine marasa tsari sun toshe hanyoyin ruwa na Kogin Dingi, wanda ya tunbaza har ya yi ambaliya sakamakon ruwan saka kamar da bakin kwarya. Rashin hanyoyin madatsun ruwa sun kara yin tasirin ambaliyar ruwan a garin.

“‘Yan Nijeriya za su iya tuna cewa Ma’aikatar Ruwa ta Tarayya, ta hanyar Hukumar Kula da Madatsun Ruwa ta Nijeriya (NIHSA), a cikin hasashen ambaliyar ruwa na 2025, a ranar 10 ga Afrilu, 2025, ta yi hasashen ambaliyar ruwa a cikin kananan hukumomi 19 na Jihar Neja, ciki har da karamar hukumar Mokwa.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: ambaliyar ruwa

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaba Tinubu Ya Karrama Bill Gates Da Lambar Girmamawa Ta CFR

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya karrama daya daga cikin  masu kamfanin Microsoft, Bill Gates, da lambar girmamawa ta kasa — Commander of the Order of the Federal Republic (CFR), inda ya jaddada cewa Gates ya kasance abin koyi ga shugabanni a fadin duniya saboda yadda yake taimaka wa talakawa da masu bukata ta musamman.

Shugaban ya kuma bayyana cewa Mista Gates, wanda shi ne Shugaban Gidauniyar Melinda da Gates, ya bada gudummawa a fannonin kiwon lafiyar mata, noma da bincike kan cututtuka masu yaduwa.

Ya gode wa Bill Gates bisa gudummawar da yake bayarwa a duniya, musamman wajen saukaka rayuwa da kare lafiyar masu rauni da wadanda ke cikin bukata.

Ministan Lafiya da Ci gaban Jama’a, Farfesa Ali Pate, ya ce karramawar da aka yi wa Mista Gates ta cancanta kwarai,  idan aka yi la’akari da irin gagarumar rawar da ya taka a ci gaban Najeriya.

Farfesa Pate ya bayyana cewa taimakon da Gidauniyar Bill da Melinda Gates ta bayar ya taimaka sosai wajen kawar da cutar shan inna (polio) a kasar.

Yayin da yake gode wa Shugaban Kasa bisa karramawar CFR, Mista Gates ya ce yaki da cutar shan inna daya ce daga cikin mafi wahala da Gidauniyarsu ta yi, sai dai hakan ya sa su hada kai da sarakunan gargajiya don cimma nasara.

Ya bayyana cewa Gidauniyar ta kaddamar da allurar rigakafin cutar HPB don rage mace-macen mata kimanin 7,000 a shekara sakamakon cutar sankarar mahaifa.

Mista Gates ya bayyana cewa allura guda daya kacal da ake bai wa ‘yan mata masu shekaru 9 zuwa 14 na iya basu kariya na daga cutar.

Gates ya tabbatar wa Shugaban Kasa cewa zai ci gaba da jajircewa wajen inganta lafiya a Najeriya, inda ya ce yana da niyyar amfani da dukiyarsa gaba daya wajen wannan aiki cikin shekaru ashirin masu zuwa.

Aliko Dangote, Shugaban Kamfanin Dangote, Ministan Harkokin Musamman da Hulda tsakanin Gwamnati, Zephaniah Jisalo, manyan jami’an Gidauniyar Gates, da Dakta Ayuba Burki Gufwan, Sakataren Gwamnati na Hukumar Kula da Masu Bukata ta Musamman na Kasa, na daga cikin wadanda  suka halarci bikin karramawar.

Daga Bello Wakili

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
  • Tsohon Alkalin Alkalan Najeriya, Lawal Uwais ya rasu
  • Wani mutum ya mutu a cikin rijiya a Kano
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus
  • Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa
  • Barazanar Yajin Aiki: Abuja da wasu jihohi 3 za su faɗa cikin duhu
  • HOTUNA: Yadda ambaliya ta raba mutane da muhallansu a Mokwa
  • Ambaliyar Mokwa: An gano gawar yara 7, jama’a na neman agaji
  • Shugaba Tinubu Ya Karrama Bill Gates Da Lambar Girmamawa Ta CFR