Afirka Tana Shirin Samar Da Maganin Kwalara Da Kanta
Published: 6th, June 2025 GMT
Shugabannin nahiyar Afirka sun tattauna hanyoyin samar da maganin kwalara a cikin nahiyar.
An tattauna wannan batun ne dai a yayin taron da aka yi ta hanyar bidiyo daga nesa akan hanyoyin magance cutuka mabanbanta da su ka hada da riga-kafi.
Wadanda su ka halarci tattaunawar ta bidiyo sun hada shugabannin kasashen Angola, Namibia, Malawi da kuma DRC.
Shugaban kasar Zambia Hakayinde Hichilema ya bayyana cewa; Da akwai bukatar nahiyar Afirka ta fara samar da magunguna cikin gaggawa tare da dogaro da nahiyar wajen samar da kudaden da ake bukata domin yin hakan, saboda kaucewa dogaro da waje.”
Haka nan kuma shugaban kasar ta Zambia ya ce: Saboda kwalara idan ta barke ba ta san iyakar kasashe ba, ya kamata mu yi aiki tare da kuma samar da tsarin yin gargadi na gaggawa a tsakanin kasashen makwabta.”
Shi kuwa shugaban kasar Angola João Lourenço, wanda kuma shi ne yake rike da kambun jagorancin kungiyar nahiyar Afirka, ya bayyana cewa: ” Cutar kwalara ta fi karfin a dauke ta a matsayin wani yanayi na gaggawa da yake bijirowa a fagen kiwon lafiya, tana a matsayin kaulabale ne mai girma dake hana ci gaba na tattalin arziki da bunkasar al’umma a nahiyar ta Afirka.”
Shi kuwa shugaban hukumar lafiya ta duniya : Adhanom Gibisos cewa ya yi; A cikin wannan shekarar ta 2025 a cikin nahiyar Afirka ne za yi kaso 1/3 na dukkanin kwalarar da za ta barke a duniya, kuma a cikin nahiyar ne dai za a sami mutuwar kaso 99% na jumillar wadanda cutar za ta kaseh a duniya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: nahiyar Afirka
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Cewa: Amurka Da Isra’ila Suna Da Mugun Nufi Kan Iran Da Kasashen Musulmi
Shugaban kasar Iran ya jaddada cewa: Amurka da haramtacciyar kasar Isra’ila suna da mugun nufi kan Iran da kasashen musulmi
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya jaddada cewa: Amurka da haramtacciyar kasar Isra’ila na da mugun nufi kan Iran da kasashen musulmi.
A yayin wani jawabi da ta gabatar a wajen juyayin tunawa da rasuwar Imam Khumaini {r.a}, Pezeshkian ya ce: Haramtacciyar kasar Isra’ila ba za ta iya aikata wani aiki hauka da wauta ba, idan kasashen musulmi suka hada kansu.
Pezeshkian ya kara da cewa: Wadanda ke da’awar kare hakkin bil’adama suna kare “haramtacciyar kasar Isra’ila” mai laifi, kuma suna ci gaba da adawa da shirin makamashin nukiliyar Iran na zaman lafiya.
Ya ci gaba da cewa: “Babu mutum mai ‘yanci da zai yarda da zalunci da girman kai, kuma Iran ba zata yarda da shi ba.”
Pezeshkian ya bayyana cewa: “Za su dakile duk wani makirce-makircen abokan gaba kuma ba za su taba yin watsi da ‘yancinsu na nukiliya da na kimiyya ba.”