Afirka Tana Shirin Samar Da Maganin Kwalara Da Kanta
Published: 6th, June 2025 GMT
Shugabannin nahiyar Afirka sun tattauna hanyoyin samar da maganin kwalara a cikin nahiyar.
An tattauna wannan batun ne dai a yayin taron da aka yi ta hanyar bidiyo daga nesa akan hanyoyin magance cutuka mabanbanta da su ka hada da riga-kafi.
Wadanda su ka halarci tattaunawar ta bidiyo sun hada shugabannin kasashen Angola, Namibia, Malawi da kuma DRC.
Shugaban kasar Zambia Hakayinde Hichilema ya bayyana cewa; Da akwai bukatar nahiyar Afirka ta fara samar da magunguna cikin gaggawa tare da dogaro da nahiyar wajen samar da kudaden da ake bukata domin yin hakan, saboda kaucewa dogaro da waje.”
Haka nan kuma shugaban kasar ta Zambia ya ce: Saboda kwalara idan ta barke ba ta san iyakar kasashe ba, ya kamata mu yi aiki tare da kuma samar da tsarin yin gargadi na gaggawa a tsakanin kasashen makwabta.”
Shi kuwa shugaban kasar Angola João Lourenço, wanda kuma shi ne yake rike da kambun jagorancin kungiyar nahiyar Afirka, ya bayyana cewa: ” Cutar kwalara ta fi karfin a dauke ta a matsayin wani yanayi na gaggawa da yake bijirowa a fagen kiwon lafiya, tana a matsayin kaulabale ne mai girma dake hana ci gaba na tattalin arziki da bunkasar al’umma a nahiyar ta Afirka.”
Shi kuwa shugaban hukumar lafiya ta duniya : Adhanom Gibisos cewa ya yi; A cikin wannan shekarar ta 2025 a cikin nahiyar Afirka ne za yi kaso 1/3 na dukkanin kwalarar da za ta barke a duniya, kuma a cikin nahiyar ne dai za a sami mutuwar kaso 99% na jumillar wadanda cutar za ta kaseh a duniya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: nahiyar Afirka
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: Yadda Tsarin Ilimi Ke Karya Gwiwar ’Yan Najeriya
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Yan Najeriya da dama ne dai da suka yi ilimin zamani dole ta sa suka rungumi sana’o’in da a baya ake ganin na kaskantattu ne don su samu na sakawa a bakin salati.
Mai yiwuwa hakan ne ya sa wasu, musamman matasa, suka yanke kauna da cewa shafe lokaci ana karatun kan iya taimaka wa mutum magance bukatunsa nay au da kullum.
NAJERIYA A YAU: Yadda Cutar Amosanin Jini Ta Hana Ni Cimma Buri Na DAGA LARABA: Ko Kare Kai Daga Harin ‘Yan Ta’adda Zai Kawo Karshen Matsalar Tsaro?Wannan shi ne batun da shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.
Domin sauke shirin, latsa nan