A shekara 25, na kashe tiriliyan 161 wajen inganta lafiya a Afirka – Bill Gates
Published: 5th, June 2025 GMT
Attajirin nan na duniya dan asalin kasar Amurka, Bill Gates, ya ce a shekara 25 da gidauniyarsa ta yi da kafuwa, ya kashe Dalar Amurka biliyan 100, kwatankwacin Naira tiriliyan 161 wajen inganta kiwon lafiya a nahiyar Afirka.
Attajirin ya bayyana hakan ne a Legas yayin wani taro da gidauniyarsa ta Gates Foundation ta shirya mai taken Goalkeepers, ranar Laraba.
Ya ce gidauniyar ta fara aiki ne a shekara ta 2000, kuma babban makasudinta shi ne ganin an rage samun mace-macen kananan yara a fadin duniya, musamman a Afirka.
Kotu ta aike da ɗan Tiktok gidan yari kan yin shigar mata a Kano NAJERIYA A YAU: Yadda Mayar Da Unguwa Mayanka Ke Shafar Lafiyar Al’ummaBill Gates ya ce, “Ganin haka ne ya sa na yi nazari na ce shin mutane suna mayar da hankalinsu wajen ganin an samar wa da wasu ba’arin mutane magungunan da yankunansu ke bukata, alal misali a bangaren zazzabin cizon sauro (maleriya), sai na gano babu.
“Wannan ne ya kasance alkiblar gidauniyar Gates Foundation. Sama da kaso 70 cikin 100 na abin da nake kashewa, Dala biliyan 100, a bangaren lafiya na duniya suka tafi, kuma a tsawon wadannan shekaru 25, mun inganta alakarmu da kasashen Afirka da dama.
“A nan Najeriya muna da abokan hulda masu dadin mu’amala da suka fahimci hanyoyin da za mu bi wajen taimaka wa gwamnati,” in ji shi.
Ya kuma ce inganta harkar lafiya kan taimaka wa kasa wajen samun ci gaban tattalin arziki ta yadda za ta iya dogaro da kanta.
Mamallakin kamfanin Microsoft din ya kuma bayyana kyakkyawan fatan cewa za a samu raguwar yawan mace-macen kananan yara da kaso 50 cikin 100 daga adadin yara miliyan biyar din da yanzu haka ake samu a fadin duniya.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
Cikin jadawalin GII na 2025, kasashe masu karanci da matsakaicin kudin shiga 17, sun taka rawar gani fiye da yadda aka yi hasashe, bisa matsayin ci gabansu, yayin da kasashen Afirka dake kudu da hamadar Sahara ke kan gaba, cikin kasashe mafiya samun ci gaban kirkire-kirkire, inda kasashen Afirka ta Kudu, da Senegal da Rwanda ke kan gaba a jerin kasashen shiyyar. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp