Attajirin nan na duniya dan asalin kasar Amurka, Bill Gates, ya ce a shekara 25 da gidauniyarsa ta yi da kafuwa, ya kashe Dalar Amurka biliyan 100, kwatankwacin Naira tiriliyan 161 wajen inganta kiwon lafiya a nahiyar Afirka.

Attajirin ya bayyana hakan ne a Legas yayin wani taro da gidauniyarsa ta Gates Foundation ta shirya mai taken Goalkeepers, ranar Laraba.

Ya ce gidauniyar ta fara aiki ne a shekara ta 2000, kuma babban makasudinta shi ne ganin an rage samun mace-macen kananan yara a fadin duniya, musamman a Afirka.

Kotu ta aike da ɗan Tiktok gidan yari kan yin shigar mata a Kano NAJERIYA A YAU: Yadda Mayar Da Unguwa Mayanka Ke Shafar Lafiyar Al’umma

Bill Gates ya ce, “Ganin haka ne ya sa na yi nazari na ce shin mutane suna mayar da hankalinsu wajen ganin an samar wa da wasu ba’arin mutane magungunan da yankunansu ke bukata, alal misali a bangaren zazzabin cizon sauro (maleriya), sai na gano babu.

“Wannan ne ya kasance alkiblar gidauniyar Gates Foundation. Sama da kaso 70 cikin 100 na abin da nake kashewa, Dala biliyan 100, a bangaren lafiya na duniya suka tafi, kuma a tsawon wadannan shekaru 25, mun inganta alakarmu da kasashen Afirka da dama.

“A nan Najeriya muna da abokan hulda masu dadin mu’amala da suka fahimci hanyoyin da za mu bi wajen taimaka wa gwamnati,” in ji shi.

Ya kuma ce inganta harkar lafiya kan taimaka wa kasa wajen samun ci gaban tattalin arziki ta yadda za ta iya dogaro da kanta.

Mamallakin kamfanin Microsoft din ya kuma bayyana kyakkyawan fatan cewa za a samu raguwar yawan mace-macen kananan yara da kaso 50 cikin 100 daga adadin yara miliyan biyar din da yanzu haka ake samu a fadin duniya.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Kamfanonin lantarki ya zu katse wuta kan bashin N5.2trn da suke bin gwamnati 

Kamfanonin wutar lantarki sun yi barazanar katse wutar a fadin Najeriya saboda tarin bashin da ya haura Naira tiriliyan 5.2 da suke bin gwamnati.

Taurin bashin, wanda ke barazana ga ci gaba da ayyukan kamfanoni, ya hada da Naira tiriliyan 1.2 na wutar da aka samar a watanni shidan farkon shekarar 2025, da Naira tiriliyan 2 daga 2024, da kuma bashin da aka gada tun daga 2015 wanda ya kai Naira tiriliyan 1.9.

Shugabar ƙungiyar kamfanonin samar da wutar lantarki, Dakta Joy Ogaji, ta bayyana cewa kamfanonin sun daɗe suna nuna kishin ƙasa ta hanyar ci gaba da samar da wuta duk da rashin biyan su kuɗaɗensu, amma yanzu sun gaji.

Ta bayyana cewa kudin da ake kashewa wajen samar da wuta a kowane wata yana kaiwa Naira biliyan 250, amma Gwamnatin Tarayya ta ware Naira biliyan 900 kacal a kasafin kuɗin 2025, kuma har zuwa yau ba a samu cikakken tabbacin samun wannan kuɗin ba.

An rufe masana’antu 1,724 bisa rashin bin dokokin aiki a Guinea NAJERIYA A YAU: Yadda tsadar taki ke hana noman masara da shinkafa

Ministan Makamashi, Adebayo Adelabu, ya bayyana cewa gwamnati tana ƙoƙarin rage wani ɓangare na bashin, amma har yanzu ba a bayyana yadda hakan zai faru ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • WFP zai dakatar da tallafin abinci da kiwon lafiya a Nijeriya
  • Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne
  • UNICEF Ya Bukaci Jihar Kano Ta Bai Wa Yara Muhimmanci A Kasafin Kudi
  • Sheikh Qasem: Nuna Halin Ko In-Kula Na Duniya Ne Ya Jawo Kisan Kiyashi A Gaza
  • Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu
  • UNICEF na zargin Gwamnatin Nijeriya da cin zarafin ƙananan yara
  • Kamfanonin lantarki za su katse wuta kan bashin N5.2trn da suke bin gwamnati 
  • Kamfanonin lantarki ya zu katse wuta kan bashin N5.2trn da suke bin gwamnati 
  • Hukumar Kashe Gobara Ta Jihar Kwara Ta Taimaka Wajen Hana Lalacewar Wani Bene A Ilorin
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce; Iran Ba Zata Bar Tace Sinadarin Uranium Ba