Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta jaddada cewa: Zata mayar da martani mai gauni kan yadda ake siyasantar da batun nukiliya a cikin kwamitin gwamnonin cibiyar IAEA

Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran mai kula da harkokin shari’a da na kasa da kasa Kazem Gharibabadi ya jaddada cewa: Idan aka mayar da batun Iran na nukiliya siyasa a taron kwamitin gwamnonin cibiyar IAEA, bai kamata daya bangaren ya sa ran Iran za ta ci gaba da yin aiki da cikakken kamun kai ba tare da mayar da martani ba.

Maimakon haka, Iran za ta gudanar da mu’amalarta da siyasarta daidai da halayensu da manufofinsu.

A cikin wata sanarwa da ya fitar ta gidan talabijin na Iran a yammacin jiya Talata, dangane da matsayin Jamhuriyar Musulunci ta Iran kan rahoton baya-bayan nan da babban darektan hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya Rafa’el Grossi ya gabatar, wanda ya haifar da cece-kuce game da wani kuduri mai tsauri kan Iran a taron kwamitin gwamnonin da za a yi a mako mai zuwa, Gharibabadi ya ce: Jamhuriyar Musulunci ta Iran mamba ce ta yarjejeniyar hana kera makamin nukiliya da yaduwarta, kuma tana yin riko da dokokin da yarjejeniyar ta cimma tare da karewa.

Ya kara da cewa: “Iran ta aiwatar da alkawuran da ta dauka tare da sauke nauyin da ya rataya a wuyarta. Ko da yake ya kamata hukumar ta IAEA ta kasance kungiya ce ta fasaha da doka, amma ra’ayoyin siyasa suna yin tasiri kanta.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Nukiliya : Iran za ta bayar da amsa ga shawarar Amurka cikin kwanaki masu zuwa

Ministan harkokin wajen kasar Abbas Araghchi ya sanar da cewa, nan da kwanaki masu zuwa Iran za ta mayar da amsa kan shawarar da Amurka ta gabatar kan shirin nukiliyar kasar na zaman lafiya.

A cewarsa, shawara da Amurka ta gabatar tana bukatar zurfafa bincike.

M. Araghchi, ya bayyana hakan ne ziyarar da yake a birnin Beirut, na kasar Lebanon inda ya jaddada cewa, amsar da Iran za ta mayar zata kasance bisa tsarin Jamhuriyar Musulunci ta Iran da manufofinmu da kuma kare muradun al’ummar Iran.

Ya nanata cewa inganta makamashin Uranium tamkar “jan layi” ne ga Iran, yana mai cewa Tehran ba ta bukatar neman izini daga kowa don ci gaba da ayyukanta da suka dace da shari’a kuma halaliyarta.

Ya ce inganta sinadarin Uranium ya zama abin alfahari ga al’ummar Iran kuma wannan nasara ta ilimi ta samo asali ne daga kokari da basirar masana kimiyyar Iran, kuma ba abu ne mai sauki da za a yi watsi da ita.

Araghchi ya kuma tunatar da cewa, Iran ta ta sha wahala sosai fiye sakamakon shekaru 20 na takunkumin tattalin arziki mai tsanani da Amurka ta kakaba, da kuma kisan wasu masana kimiyyar nukiliyarta tun farkon shekarun 2010, wanda jami’an gwamnatin Isra’ila suka shirya.

Ministan harkokin wajen na Iran ya kara da cewa sama da Iraniyawa miliyan daya ne ke bukatar magunguna da cibiyar bincike ta Tehran ta samar, don haka ci gaba da sarrafa sinadarin Uranium a Iran ya zama wajibi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ali Shamkhani: Iran Ba Zata Taba Saryar Da Hakkinta Na Makamashin Nukliya Ba
  • Araghchi : Babu wata tattaunawa idan ba zamu tace uranium ba
  • Amurka ta sake yin watsi da kiran tsagaita a wuta Gaza
  • Babban Zauren MDD Ta Zabi Kasashen Congo Da Liberian Na Zama Mambobi A Kwamitin Tsaro
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Jaddada Hakkin Iran Na Tace Sinadarin Uranium
  • Nukiliya : Iran za ta bayar da amsa ga shawarar Amurka cikin kwanaki masu zuwa
  • Medvedev : babu makawa Rasha za ta mayar da martani mai zafi ga hare-haren kyiv
  • Iran ta bukaci hadin kan al’ummar Lebanon wajen warware matsalolin kasar
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Soki Rahoton Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Ta Duniya Kan Kasarsa