Irin manufar bude kofa da gyare-gyare ta kasar Sin duniya da jama’arta suka fi bukata, domin ita ce za ta bada damar samun dunkulewar duniya da ci gabanta kamar yadda ake fata, har ma da kai wa gina duniya mai kyakkyawar makoma ga dukkannin dan adam. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku.

Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka ta sake yin watsi da kiran tsagaita a wuta Gaza

Amurka ta sake hana kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya kiran tsagaita bude wuta da kuma kai agajin jin kai a Gaza.

Wannan hawa kujerar na-ki shi ne irinsa na farko na sabuwar gwamnatin Trump kuma yana zuwa ne a daidai lokacin da Isra’ila ke fuskantar matsin lamba daga kasashen duniya kan ci gaba da yakin da takeyi a gaza dama hana shigar da kayan agaji.

Daftarin kudurin da aka gabatar wa kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya a ranar Laraba ya bukaci “a gaggauta tsagaita wuta na dindindin” da kuma sakin wadanda aka yi garkuwa da su ba tare da wani sharadi ba.

Kudirin da kasashe 10 wadanda ba mambobin kwamitin na dindindin ba suka gabatar, ya samu sahalewa daga kasashe 14, yayin da Amurka ta yi fatali da shi.

Kafin kada kuri’ar, Amurka ta ce “kudirin zai wargaza kokarin diflomasiyya na cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta gaskiya, kuma zai karfafa wa Hamas,” ne in ji jakadiyar Amurka a Majalisar Dinkin Duniya, Dorothy Shea.

Jakadan Falasdinawa a Majalisar Dinkin Duniya Riyad Mansour ya bukaci MDD da ta dauki mataki.

Wannan matakin na ranar Laraba ya kasance karo na shida da Amurka ke toshe kudurin tsagaita wuta a Gaza tun watan Oktoban shekarar 2023.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore
  • Bikin Bukin Sallar Da Malta Guinness
  • Amurka ta sake yin watsi da kiran tsagaita a wuta Gaza
  • Maniyyata na hawan Arfa a kasar Saudiyya
  • Trump ya haramtawa ‘yan kasashen duniya 12 shiga Amurka
  • Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai
  • Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 
  • Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG
  • Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya