Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus
Published: 3rd, June 2025 GMT
Wasu kuma sun ce akwai rashin jituwa tsakanin Gwamnan da mahaifinsa, Oba Akinruntan.
Bayan saukar Akinruntan, an zaɓi Ololade Gbegudu daga Okitipupa a matsayin sabon mataimakin kakakin majalisar.
Gbegudu, mai shekara 42, ya riƙe muƙamin shugaban kwamitin tsaro da ci gaban al’umma a majalisar kafin wannan sabon muƙamin.
Oluwatoyin James daga Akoko ta Arewa Maso Gabas ne, ya ayyana sunansa, yayin da Chris Aiyebusiwa daga Okitipupa I ya mara masa baya.
Haka kuma, tsohon jagoran majalisar, Ogunmolasuyi daga Owo I, ya sauya wajen aiki da Olatunji Oshati daga mazaɓar Ose, wanda yanzu shi ne sabon shugaban masu rinjaye.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Murabus
এছাড়াও পড়ুন:
Sabon Firay Ministan Sudan Ya Bukaci Kasashen Dake Taimaka Wa “RSF” Da Su Daina
Sabon fira ministan kasar Sudan Kamil Idris ya yi kira ga kasashen waje masu taimaka wa dakarun daukin gaggawa “RSF” da su kawo karshen taimakon da suke bawa masu aikata laifi.”
Idris wanda yake jawabin bayan kama aiki a jiya ya ce; Jami’an tsaro da kuma mahukuntan kasar ta Sudan suna da cikakken goyon baya a kasar don kawo karsehn ‘yan tawaye, masu dauke da makamai.”
Idris ya kuma ce; A shirye yake ya yi wa kasa aiki a cikin kekyawar anniyya da kwazo.”
Gwamantin kasar Sudan dai tana zargin Hadaddiyar Daular Larabawa da taimaka wa dakarun kai daukin gaggawa “RFS” wacce ta dauki shekaru biyu tana fafatawa da sojojin kasar.
Wasu daga cikin kasashen da Sudan take zargi da hannu a tawayen na “RSF” sun hada da Chadi, Libya da Sudan Ta Kudu.
Wasu rahotannin suna nuni da cewa, suna bawa wannan kungiyar makamai ne ta kan iyakokin da su ka hada wadannan kasashe da Sudan.
Tun barkewar yakin basasa a kasar Sudan a ranar 15 ga watan April 2023, zuwa yanzu adadin mutanen da su ka rasa rayukansu sun kai 24,000, yayin da wasu fiye da miliyan 14 su ka zama ‘yan gudun gijira, miliyan 4 daga cikinsu sun fice daga kasar, zuwa kasashen makwabta.